fidelitybank

Man Fetur na ‘yan Najeriya ne ban a ‘yan Kudu ba – Obasanjo

Date:

Tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo ya ce, man fetur tare da sauran albarkatun fadin kasar nan dukkan su na ‘yan Najeriya ne, ba wain a iya wani yankin ba.

Obasanjo ya bayyana haka ne a wani martani da ya mayar wa fitaccen dattijon nan na yankin Naija Delta, Cif Edwin Clark, wanda ya zargi Obasanjo da nuna halin ko-in-kula game da illolin da hakar mai a yankin na su ya haddasa.

Wasu rahotanni sun nuna cewa Clark, a cikin wata wasika da ya rubuta, yana zargin tsohon shugaban kasar ya nuna kiyayya ga masu fafutukar mallakar albarkatun kasar da a ka samu a yankunan su.

Sai dai a martanin da ya mayar, Obasanjo ya ce, a iya saninsa albarkatun kasar nan da a ka hako a Najeriya mallakin dukkanin ‘yan kasar nan ne ba na mutanen yankunan da a ka same su ba. A cewar BBC.

Ya kara da cewa”Ba zai yiwu a samu kasashe biyu a cikin kasa daya ba, ya na mai cewa, a iya fahimtarsa Cif Clark ya na magana ne a kan samar da wata kasa a cikin Najeriya idan har ya na so a baiwa Naija Delta damar mallakar albarkatun kasar da a ka samu a yankin”.

A cewarsa, “Kundin tsarin mulkin Najeriya, wanda ya yarda cewa zinaren da a ka samu a Zamfara, ko “zinaren da a ka samu a Ilesha da ke Jihar Osun, da kuma ma’adinin lead da ke Jihar Ebonyi” shi ne kuma ya bayyana cewa fetur din da a ka samu a Naija Delta duka na ‘yan kasar ne”.

Obasanjo ya kara da cewar,”Dukkan mutanen da su ka kulla yarjejeniyar sayen danyen man fetur sun yi ne da Najeriya a matsayin kasa ba da yankin Naija Delta ba, inna mai jaddada cewa, Najeriya dunkulalliyar kasa ce da babu wanda ya isa ya raba ta, ciki har da raba albarkatun da ke cikinta”.

A cewarsa: “Idan akwai wata barazanar tsaro a kowanne bangare na Najeriya a yau, ciki har da yankin Naija Delta, sojojin Najeriya ne tare da tallafin wasu jami’an tsaro, a matakin gwamnatin tarayya, za su yi raddi kan hakan”. Inji Obasanjo.

Masu fafutuka a yankin Naija Delta sun dade suna kokarin ganin sun mallaki fetur din da ake hakowa a yankinsu, inda a wasu lokutan lamarin yakan kai ga kashe-kashe da satar ma’aikatan man fetur.

 

 

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp