fidelitybank

Tsaro: ‘Yan Katsina ku mallaki Bindigar kan ku -Masari

Date:

Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari, ya ja hankalin al’ummar jihar da su yi amfani da makamai domin tunkarar ‘yan bindiga da ke addabar su.

A cewar gwamnan yayin zantawa da manema labarai ya ce, jami’an tsaro kadai ba za su iya magance matsalar rashin tsaro a jihar ba.

Da ya ke jawabi yayin wani taron manema labarai a Katsina, Masari ya jaddada cewa yawan jami’an tsaro a jihar bai isa a shawo kan lamarin ba.

“A Musulunci ya halatta mutum ya kare kansa daga harin. Dole ne mutum ya tashi ya kare kansa, da iyalansa, da dukiyarsa. Idan ka mutu ka na ƙoƙarin kare kanka, za a ɗauke ka a matsayin shahidi. Abin mamaki ne yadda dan fashi zai mallaki bindiga alhali mutumin kirki da ke kokarin kare kansa da iyalansa ba shi da ita”.

Ya kuma yi nuni da cewa gwamnatin jihar za ta taimaka wa masu shirin mallakar makamai, domin kawo karshen matsalar ‘yan fashi da makami a jihar.

“Za mu goyi bayan wadanda su ka zo da shirin sayo makamai, saboda mazauna yankin na bukatar su kara kaimi ga kokarin hukumomin tsaro. Wadannan mutane (jami’an tsaro) ba su da yawan da za su kare jama’a.

“Lokacin da Shugaba Buhari ya zo, har ma ya yi kokarin kara yawan jami’an tsaron mu, amma abin bai wadatar ba. Ku lissafa kanku, ‘yan sanda nawa mu ke da su a kasar nan? Sojoji nawa mu ke da su?

“Ko da mu ka ce kowane dan sanda ya koma jiharsa, ba zai wadatar ba. Domin haka, idan mu ka ninke hannu mu ka yanke shawarar yin komai, za mu fi shan wahala”. Inji shi.

Masari ya ce,”‘Yan sanda za su yi rijistar duk bindigogin da mazauna garin su ka saya, domin tabbatar da an yi amfani da su yadda ya kamata. Katsina, kamar sauran jihohin Arewa maso Yamma, Zamfara, Kaduna, Sokoto, da Kebbi, sun sha fama da hare-haren kungiyoyin ‘yan ta’adda”. A cewar Masari

Rahotanni na nuni da cewa, Daruruwan mutane ne a ka kashe ko kuma a ka yi garkuwa da su a Katsina cikin wannan shekara tare da raba dubbai daga gidajen su.

 

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp