Jigon jam’iyyar APC na kasa, kuma tsohon gwamnan jihar Legas, Sanata Bola Tinubu, ya bayyana bayar da gudunmuwar Naira miliyan 50 ga al’ummar Zamfara da wasu ‘yan bindiga suka kai wa hari a kwanakin baya.
Tinubu ya sanar da tallafin ne jim kadan bayan ya mika ta’aziyyarsa ga gwamna Bello Matawalle a garin Gusau na jihar Zamfara a ranar Alhamis.
Shugaban jam’iyyar APC na kasa ya yi kira da a dage da addu’a, domin shawo kan matsalar rashin tsaro a jihar.
“Zan iya yin addu’a ga mutane daga ko’ina, amma zuwa da kaina ya na da mahimmanci.
“Za a yi galaba a kan makiya ilimi, Boko Haram da sauran muggan laifuka ta hanyar sadaukar da kai ga bil’adama.
“Mu na addu’a ga kasar baki daya ta zauna lafiya, kuma idan makiya suka ki hana kashe-kashen da ake yi, za mu kawar da su”. A cewar Tinubu.