‘Yan ta’addan da suka kai hari gidan ajiya da gyaran hali na Medium Security da ke Jos a Jihar Filato a ranar Lahadin da ta gabata a yanzu haka an yi musu kawanya a cikin gidan.
Hakan ya fito ne ta cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Francis Enobore, ya fitar a daren Lahadi.
Ya kuma ce, “Mun fuskanci harin da wasu ‘yan bindiga suka kai wa cibiyar, wanda su na da yawa da manyan makamai a hannun su. Duk da cewa sun samu shiga cikin gidan, amma duk da haka sun makale a ciki, inda nan take aka tara maza daga jami’an tsaro ‘yan uwa, domin su taimaka wa masu gadin da ke dauke da makamai, domin killace katangar da ma yankin baki daya”. Inji Francis.
Rahotanni ya nuna cewa, maharan sun shiga gidan ajiya da gyaran hali da misalin karfe Biyar da Ashirin na yamma, inda nan take suka nufi babbar kofar shiga gidan, inda su ka yi artabu da jami’an rundunar da ke dauke da makamai kafin su kutsa cikin farfajiyar gidan.
A na ci gaba da shawo kan lamarin, yayin da maharan su ka yi masayan harsashai da tawagar jami’an tsaro.