fidelitybank

Tsaro: ‘Yan ta’adda sun aike da wasika ga mabioya addinin Kirista a Zamfara

Date:

Wasu gungun ‘yan bindiga sun rubuta wasika ga mabiya addinin Kirista a jihar Zamfara da ke Arewa Maso yammacin Najeriya cewa da su rufe coci-coci ko kuma su fuskanci munanan hare-hare.

A tattaunawa da Saharareporters, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Mohammed Shehu, ya ce ‘yan sanda sun san da wasikar barazanar, kuma suna kan gaba wajen shawo lamarin.

Ya ce, “Eh, zan iya tabbatar da cewa gaskiya ne, an aike da wasikar barazanar ga Kiristocin Jihar Zamfara su daina ibada da kuma rufe Coci. A gaskiya ‘yan sanda sun sanar da shugabannin addinin Kirista game da barazanar. Haka zalika kwamishina ‘yan sanda ya gayyaci shugabannin kungiyar Kiristocin Najeriya ta CAN a jihar, domin tattauna matakan tsaro a kan lamarin, dangane da haka, kwamishinan ya samar da wata tawaga ta musamman da za ta rika sintiri tare da kare masu ibada, musamman a ranar Lahadi. Bugu da ƙari, an tura ma’aikatan sanye da kayan aiki, domin tattara bayanan sirri da kuma bankado waɗanda ke da hannu a cikin wasikar barazanar,” in ji shi.

A ranar Lahadin da ta gabata ne wani daga cikin shugaban addinin Kirista da ya nemi a sakaya sunansa ya bukaci mabiya addinin Kirista a sassan duniya da su yi addu’a kan halin da suke ciki a Zamfara da sauran sassan Arewacin Najeriya.

 

 

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp