Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya domin jana’izar marigayi, fitaccen ɗan kasuwa kuma dattijo, Alhaji Aminu Alhassan Dantata a birnin Madina.
Marigayi Dantata ya rasu ne a Abu Dhabi, babban birnin Hadaddiyar Daular Larabawa, a ranar Asabar yana da shekara 94.
Tawagar ta bar Najeriya da yammacin Lahadi, inda ta isa Madina da safiyar Litinin.
Tawagar na ƙarƙashin jagorancin ministan tsaro kuma tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar.
Sauran mambobin tawagar sun haɗa da ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, Lateef Fagbemi (SAN) da ministan yaɗa labarai, Alhaji Mohammed Idris, da ƙaramin ministan gidaje da raya birane, Hon. Yusuf Abdullahi Ata da dai sauran su.
Akwai kuma manyan malamai a cikin tawagar da suka haɗa da sheikh Aminu Daurawa da Dr Bashir Aliyu Umar da kuma Khalifa Abdullahi Muhammad.