Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa game da rasuwar fitaccen mai taimakon jama’a, Alhaji Aminu Dantata wanda ya rasu a ranar Juma’a.
Hakan na kunshe ne a cikin sakon ta’aziyyar mai dauke da sa hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Hon. Eseme Eyiboh, ranar Lahadi.
Akpabio ya bayyana marigayi Dantata a matsayin mutum mai kishin zuciya wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen taimakawa marasa galihu.
“Marigayi Aminu Dantata ya nuna kauna ga bil’adama ta yadda ya jajirce wajen ganin halin da talakawa da mabukata suke ciki, ayyukan taimakon sa ya kasance wanda ba za a manta da shi ba a tarihin kasarmu,” in ji Akpabio.
Ya kara da cewa ya san Dantata a matsayin mutum mai hazaka kuma mai kyauta wanda ya yi arzikinsa ta hanyar kwazo da sana’a.
Ya kara da cewa irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar Kano da Arewacin Najeriya da ma kasa baki daya na da dimbin yawa.
Shugaban majalisar dattawan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Dantata, jama’a da gwamnatin jihar Kano, da ‘yan kasuwar Najeriya.
Ya bayyana marigayi dan kasuwan a matsayin ginshiki, wanda ya cancancta, kuma mutumin da ba za a iya mantawa da shi ba a Najeriya.
“A gaskiya Marigayi Dantata cibiya ce ta kan sa, ya cancanci a yi koyi da shi kuma ya dawwama,” in ji shi.
“A madadin iyalai na, da ‘yan mazaba, da Majalisar Dattawa, da kuma daukacin Majalisar Dokoki ta kasa, ina mika ta’aziyyata ga iyalan Dantata tare da addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya ba shi Aljannar Firdausi,” sanarwar ta karkare.