fidelitybank

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Date:

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa game da rasuwar fitaccen mai taimakon jama’a, Alhaji Aminu Dantata wanda ya rasu a ranar Juma’a.

Hakan na kunshe ne a cikin sakon ta’aziyyar mai dauke da sa hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Hon. Eseme Eyiboh, ranar Lahadi.

Akpabio ya bayyana marigayi Dantata a matsayin mutum mai kishin zuciya wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen taimakawa marasa galihu.

“Marigayi Aminu Dantata ya nuna kauna ga bil’adama ta yadda ya jajirce wajen ganin halin da talakawa da mabukata suke ciki, ayyukan taimakon sa ya kasance wanda ba za a manta da shi ba a tarihin kasarmu,” in ji Akpabio.

Ya kara da cewa ya san Dantata a matsayin mutum mai hazaka kuma mai kyauta wanda ya yi arzikinsa ta hanyar kwazo da sana’a.

Ya kara da cewa irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar Kano da Arewacin Najeriya da ma kasa baki daya na da dimbin yawa.

Shugaban majalisar dattawan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Dantata, jama’a da gwamnatin jihar Kano, da ‘yan kasuwar Najeriya.

Ya bayyana marigayi dan kasuwan a matsayin ginshiki, wanda ya cancancta, kuma mutumin da ba za a iya mantawa da shi ba a Najeriya.

“A gaskiya Marigayi Dantata cibiya ce ta kan sa, ya cancanci a yi koyi da shi kuma ya dawwama,” in ji shi.

“A madadin iyalai na, da ‘yan mazaba, da Majalisar Dattawa, da kuma daukacin Majalisar Dokoki ta kasa, ina mika ta’aziyyata ga iyalan Dantata tare da addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya ba shi Aljannar Firdausi,” sanarwar ta karkare.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...
X whatsapp