fidelitybank

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Date:

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa game da rasuwar fitaccen mai taimakon jama’a, Alhaji Aminu Dantata wanda ya rasu a ranar Juma’a.

Hakan na kunshe ne a cikin sakon ta’aziyyar mai dauke da sa hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Hon. Eseme Eyiboh, ranar Lahadi.

Akpabio ya bayyana marigayi Dantata a matsayin mutum mai kishin zuciya wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen taimakawa marasa galihu.

“Marigayi Aminu Dantata ya nuna kauna ga bil’adama ta yadda ya jajirce wajen ganin halin da talakawa da mabukata suke ciki, ayyukan taimakon sa ya kasance wanda ba za a manta da shi ba a tarihin kasarmu,” in ji Akpabio.

Ya kara da cewa ya san Dantata a matsayin mutum mai hazaka kuma mai kyauta wanda ya yi arzikinsa ta hanyar kwazo da sana’a.

Ya kara da cewa irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban jihar Kano da Arewacin Najeriya da ma kasa baki daya na da dimbin yawa.

Shugaban majalisar dattawan ya mika ta’aziyyarsa ga iyalan Dantata, jama’a da gwamnatin jihar Kano, da ‘yan kasuwar Najeriya.

Ya bayyana marigayi dan kasuwan a matsayin ginshiki, wanda ya cancancta, kuma mutumin da ba za a iya mantawa da shi ba a Najeriya.

“A gaskiya Marigayi Dantata cibiya ce ta kan sa, ya cancanci a yi koyi da shi kuma ya dawwama,” in ji shi.

“A madadin iyalai na, da ‘yan mazaba, da Majalisar Dattawa, da kuma daukacin Majalisar Dokoki ta kasa, ina mika ta’aziyyata ga iyalan Dantata tare da addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya ba shi Aljannar Firdausi,” sanarwar ta karkare.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp