fidelitybank

Siyasa: Sanata ya raba motoci 50 da Babura 500 da firji 600

Date:

Sanata mai wakiltar Gombe ta Arewa a majalisar wakilai ta kasa, Sa’idu Alkali, ya raba kayan tallafi na miliyoyin Naira ga mazabar sa.

Kayayyakin da a ka raba sun hada da motoci 50, babura 500, injin dinki da firij 600, famfunan hannu na noman rani, masuskar shinkafa da sarrafa masara ga manoma 1,000 da dai sauransu, a Gombe ranar Lahadi.

Da ya ke jawabi a wajen bikin rabon kayayyakin, Sanatan ya ce, “Hakan shi ne nasa hanyar nuna jin dadi na ga al’ummar mazaba ta na ganin na cancanci wakilce su a karo na Uku a majalisar dattawa”.

Ya ce kuma ce”A cikin ayyukan mazabarsa na 2021, na gina tubalan ajujuwa da cibiyoyin kiwon lafiya, na samar da ayyukan ruwa da hanyoyin mota a fadin kananan hukumomin guda biyar da na ke wakilta, Dukku da Gombe da Kwami da Funakaye da kuma Nafada”. Inji Sanata.

A nasa jawabin, Gwamna Inuwa Yahaya ya yabawa Sanatan bisa yadda ya baiwa al’ummar mazabar sa kwarin gwiwa, sannan ya bayyana fatansa na ganin cewa abubuwan karfafawa za su yi tasiri ga rayuwar al’ummar mazabar sa.

nigeria 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...
X whatsapp