Mai kula da Masallatan Harami guda biyu, Sarki Salman ya bayyana cewa, an fara shirin kashi na biyu na muradan shekarar 2030 na Masarautar wanda ya kara kaimi ga nasarori da gyare-gyare da a ke ci gaba da yi.
Da ya ke kaddamar da ayyukan shekara ta biyu na zama na takwas na Majalisar Shoura a yammacin Larabar, Sarkin ya bayyana cewa manufar ta na da manufar tabbatar da ci gaban kasar nan da samar da makoma mai kyau ga al’ummarta ta hanyar samar da ingantaccen tsarin tattalin arziki mai ma’ana daban-daban wanda zai iya yin tasiri da sauye-sauyen duniya.
Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman ya halarci taron bude taron majalisar, wanda ya bayyana manyan alfanun da ke tattare da manyan ayyukan da suka hada da samar da guraben ayyukan yi ga Saudiyya.
Ya kuma ce, “Mun albarkaci kaddamar da ayyuka da dama da Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman ya yi tare da hangen nesa na gaba wanda ke goyon bayan dokokin Masarautar da kuma dorewarta, wadata, kirkire-kirkire, da jagoranci na kasuwanci. Waɗannan suna kawo ɗimbin guraben ayyukan yi da kuma babbar riba ga babban abin cikin gida na (GDP)”. Inji shi.
A yayin da ya ke bayyana manufofin masarautar cikin gida da waje, Sarkin ya ja hankali kan matsayin kasar Saudiyya a duniya bisa matsayinta ta na Larabawa da Musulunci, da kuma rawar da take takawa a fagen siyasar kasa da kasa, da kuma kudurin da ta dauka na kiyaye alkawuran da a ka dauka na tabbatar da tsaro da zaman lafiya da kuma kwanciyar hankali da wadata.