fidelitybank

Saudiyya ta fara shiri na 2 a kan muradan shekarar 2030

Date:

Mai kula da Masallatan Harami guda biyu, Sarki Salman ya bayyana cewa, an fara shirin kashi na biyu na muradan shekarar 2030 na Masarautar wanda ya kara kaimi ga nasarori da gyare-gyare da a ke ci gaba da yi.

Da ya ke kaddamar da ayyukan shekara ta biyu na zama na takwas na Majalisar Shoura a yammacin Larabar, Sarkin ya bayyana cewa manufar ta na da manufar tabbatar da ci gaban kasar nan da samar da makoma mai kyau ga al’ummarta ta hanyar samar da ingantaccen tsarin tattalin arziki mai ma’ana daban-daban wanda zai iya yin tasiri da sauye-sauyen duniya.

Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman ya halarci taron bude taron majalisar, wanda ya bayyana manyan alfanun da ke tattare da manyan ayyukan da suka hada da samar da guraben ayyukan yi ga Saudiyya.

Ya kuma ce, “Mun albarkaci kaddamar da ayyuka da dama da Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman ya yi tare da hangen nesa na gaba wanda ke goyon bayan dokokin Masarautar da kuma dorewarta, wadata, kirkire-kirkire, da jagoranci na kasuwanci. Waɗannan suna kawo ɗimbin guraben ayyukan yi da kuma babbar riba ga babban abin cikin gida na (GDP)”. Inji shi.

A yayin da ya ke bayyana manufofin masarautar cikin gida da waje, Sarkin ya ja hankali kan matsayin kasar Saudiyya a duniya bisa matsayinta ta na Larabawa da Musulunci, da kuma rawar da take takawa a fagen siyasar kasa da kasa, da kuma kudurin da ta dauka na kiyaye alkawuran da a ka dauka na tabbatar da tsaro da zaman lafiya da kuma kwanciyar hankali da wadata.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp