fidelitybank

Saudiyya ta fara shiri na 2 a kan muradan shekarar 2030

Date:

Mai kula da Masallatan Harami guda biyu, Sarki Salman ya bayyana cewa, an fara shirin kashi na biyu na muradan shekarar 2030 na Masarautar wanda ya kara kaimi ga nasarori da gyare-gyare da a ke ci gaba da yi.

Da ya ke kaddamar da ayyukan shekara ta biyu na zama na takwas na Majalisar Shoura a yammacin Larabar, Sarkin ya bayyana cewa manufar ta na da manufar tabbatar da ci gaban kasar nan da samar da makoma mai kyau ga al’ummarta ta hanyar samar da ingantaccen tsarin tattalin arziki mai ma’ana daban-daban wanda zai iya yin tasiri da sauye-sauyen duniya.

Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman ya halarci taron bude taron majalisar, wanda ya bayyana manyan alfanun da ke tattare da manyan ayyukan da suka hada da samar da guraben ayyukan yi ga Saudiyya.

Ya kuma ce, “Mun albarkaci kaddamar da ayyuka da dama da Yarima mai jiran gado Muhammad Bin Salman ya yi tare da hangen nesa na gaba wanda ke goyon bayan dokokin Masarautar da kuma dorewarta, wadata, kirkire-kirkire, da jagoranci na kasuwanci. Waɗannan suna kawo ɗimbin guraben ayyukan yi da kuma babbar riba ga babban abin cikin gida na (GDP)”. Inji shi.

A yayin da ya ke bayyana manufofin masarautar cikin gida da waje, Sarkin ya ja hankali kan matsayin kasar Saudiyya a duniya bisa matsayinta ta na Larabawa da Musulunci, da kuma rawar da take takawa a fagen siyasar kasa da kasa, da kuma kudurin da ta dauka na kiyaye alkawuran da a ka dauka na tabbatar da tsaro da zaman lafiya da kuma kwanciyar hankali da wadata.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Shugabannin Afrika za su halarci jana’izar Buhari

Ana sa ran wasu daga cikin shugabannin ƙasashen Afirka...

Yadda ake shirye-shiryen jana’izar Buhari a Daura

A yanzu haka dai alumma na ta tururuwa domin...

Shettima ya yi wa iyalan marigayi Muhammadu Buhari ta’aziyya a Landan

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya yi wa wasu...

Indiya na jimamin mutuwar Buhari – Modi

Firaministan India Narendra Modi, ya shiga jerin shugabanni da...

Kungiyar Gwamnoni sun bayar da hutu kan mutuwar Buhari

Ƙungiyar gwamnonin arewa maso yammacin Najeriya sun bayyana kaɗuwarsu...

Tinubu ya bayar da hutu don yin ta’azziyar Buhari

Gwamnatin tarayya ta ayyana gobe Talata, 15 ga watan...

Shettima ya isa Landan domin dawo da gawar marigayi Muhammadu Buhari

A safiyar yau Litinin ne mataimakin shugaban Najeriya Kashim...

Najeriya ta yi rashin Buhari – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana rasuwar tsohon...

Tabbas Buhari mutum ne mai kyakyawan halaye mai kishin kasa – IBB

Tsohon shugaban mulkin soji a Najeriya, Janar Ibrahim Babangida,...

Tabbas Buhari dan kishin kasa ne – Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya bayyana tsohon Shugaban Ƙasa,...

Najeriya ta yi rashin Dattijo – Atiku Abubakar

Tsohon Mataimakin Shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana Muhammadu...

Buhari ya yi rayuwa mai sauki – Tajudeen

Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya Tajudeen Abba ya miƙa ta'aziyyar...
X whatsapp