fidelitybank

Safarar mutane: Kotu ta yankewa dan kasar Kamaru hukunci a Kano

Date:

Wata babbar kotun tarayya a Kano, ta yankewa wani dan kasar Kamaru, Wamba Jean-Gaston mai shekaru 41, hukuncin daurin shekaru biyar a gidan gyaran hali, bisa samunsa da laifin safarar wasu matasa mata uku da maza hudu daga kasar Kamaru zuwa Najeriya daga nan kuma ya wuce da su Turai.

Matan uku da abin ya shafa su ne: Belinga Ovanda mai shekaru 19 da Koussene Agnes, mai shekaru 21 da Meye Uwono mai shekaru 27 yayin da mazan su ne Thomas Ange, mai shekaru 21 da Ovanda Rodrigue, mai shekaru 21 da Boris Kouass, mai shekaru 20 tare da Yannick Poudjom, mai shekaru 18.

Mai shari’a Abdullahi Muhammed-Liman ya yankewa Jean-Gaston hukunci, bayan ya amsa laifuka biyu da ake tuhumarsa da shi.

Liman ya bayyana damuwarsa kan tasirin da mai laifin ke da shi ga rashin tsaro a yankin baki daya da ya shafi kasashe da dama.

Tun da farko, Lauyan hukumar hana safarar mutane ta kasa (NAPTIP), Mista Abdullahi Babale, ya shaidawa kotu cewa, an kama wanda ake tuhuma a Kano ranar 10 ga watan Disamba, 2021.

Babale ya ce, an kama dan Kamarun ne tare da mutanen bakwai da aka kashe a kan hanyarsu ta zuwa kasar Aljeriya.

Ya ce, mai laifin ya na sarrafa takardun shiga ba bisa ka’ida ba ga wadanda aka yi safarar su zuwa kasashen Algeria da Turai ta Najeriya da Jamhuriyar Nijar, ba tare da takardar izinin zama ko biza ba.

Lauyan ya ce, laifin ya sabawa sashe na 26 (1) na dokar tilastawa mutane fataucin mutane, 2015.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

ÆŠanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon É—antakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...

Ambaliyar ruwa ta kashe mutuane takwas a Ebonyi

Ambaliya, wadda mamakon ruwan sama ya janyo, ta yi...

Bankin Duniya zai kashe wa yankin Arewa a Najeriya dala miliyan 300

Bankin Duniya ya amince da kasafin kuÉ—i dala miliyan...

Giyar mulki na kwasar Trump – ‘Yan Majalisar Democrat

'Yan Democrats a Amurka sun zargi Donald Trump da...

Kama Aminu Waziri Tambuwal da EFCC ta yi ba daidai ba ne – PDP

Jam'iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da...

An kai hari a Æ™auyuka 15 na Zamfara a mako É—aya – Rahoto

Wani rahoto da tashar Channels ta ruwaito daga cibiyar Zamfara Circle...

Jihohin Arewa huÉ—u ne suke biyan mafi Æ™arancin fansho na N32,000 – NUP

Ƙungiyar ƴan fansho na arewacin Najeriya, NUP ta ce...
X whatsapp