fidelitybank

Safarar mutane: Kotu ta yankewa dan kasar Kamaru hukunci a Kano

Date:

Wata babbar kotun tarayya a Kano, ta yankewa wani dan kasar Kamaru, Wamba Jean-Gaston mai shekaru 41, hukuncin daurin shekaru biyar a gidan gyaran hali, bisa samunsa da laifin safarar wasu matasa mata uku da maza hudu daga kasar Kamaru zuwa Najeriya daga nan kuma ya wuce da su Turai.

Matan uku da abin ya shafa su ne: Belinga Ovanda mai shekaru 19 da Koussene Agnes, mai shekaru 21 da Meye Uwono mai shekaru 27 yayin da mazan su ne Thomas Ange, mai shekaru 21 da Ovanda Rodrigue, mai shekaru 21 da Boris Kouass, mai shekaru 20 tare da Yannick Poudjom, mai shekaru 18.

Mai shari’a Abdullahi Muhammed-Liman ya yankewa Jean-Gaston hukunci, bayan ya amsa laifuka biyu da ake tuhumarsa da shi.

Liman ya bayyana damuwarsa kan tasirin da mai laifin ke da shi ga rashin tsaro a yankin baki daya da ya shafi kasashe da dama.

Tun da farko, Lauyan hukumar hana safarar mutane ta kasa (NAPTIP), Mista Abdullahi Babale, ya shaidawa kotu cewa, an kama wanda ake tuhuma a Kano ranar 10 ga watan Disamba, 2021.

Babale ya ce, an kama dan Kamarun ne tare da mutanen bakwai da aka kashe a kan hanyarsu ta zuwa kasar Aljeriya.

Ya ce, mai laifin ya na sarrafa takardun shiga ba bisa ka’ida ba ga wadanda aka yi safarar su zuwa kasashen Algeria da Turai ta Najeriya da Jamhuriyar Nijar, ba tare da takardar izinin zama ko biza ba.

Lauyan ya ce, laifin ya sabawa sashe na 26 (1) na dokar tilastawa mutane fataucin mutane, 2015.

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp