Gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa, gobara ta lalata dukiyar da ta kai ta Naira biliyan dubu 3, wato tiriliyan 3 a Najeriya.
Ministan harkokijn cikin gida, Rauf Aregbesola, ya bayyana hakan a Laraba yayin da yake sanya lambobin karin girma ga manyan shugabannin hukumar kashe gobara ta tarayyar kasar, a Abuja.
Ya ce, kasar ta tafka wannan asara ne a sanadiyyar gobara 2,845 da aka samu a sassan kasar daban-daban a shekarar da ta wuce ta 2021.
Ministan ya kuma ce,”Hukumar kashe gobara ta yi nasarar ceto kadarar da ta kai ta Naira tiriliyan 18.9 da kuma ceto rayyukan mutane 260 daga iftila’in gobara.
“Hukumar ta samu kiran gaggawa tare da kai dauki na kashe gobara har 2,845 a shekarar da ta wuce 2021”. A cewar Rauf.
Gwamnati ta kuma ce, wannan nasara ne saboda a tsakanin shekarar 2015 har zuwa yanzu, hukumar ta samu kayan aiki fiye da yadda take samu, tun lokacin da aka kafa hukumar a shekarar 1991.