Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya haramta dukannin gidajen rawa da na karuwai a jihar.
Dailypost ta rawaito cewa, Wike ya ba da wannan umarni ne a birnin Fatakwal a cikin sabon shirinsa na Yesr a Fatakwal a ranar Asabar, Wike, ya haramta gudanar da ayyukan mashahuran wuraren shakatawa na dare da su ka hada da cinikin dare da karuwanci a tituna, musamman kan titin Abacha da titunan da ke kewaye musamman a yankin Casablanca.
A cewar Wike, matakin zai “Dakatar da illolin wannan munanan ayyuka a kan ci gaban tarbiyyar yara da al’umma baki daya.”
Sai dai har yanzu ba a san tsawon lokacin da dokar za ta dore ba, amma tabbas, Gwamnan ya rage kasa da shekaru biyu a kan karagar mulki.
Wike ya kuma umurci hukumomin tsaro a jihar, da su kama tare da gurfanar da duk wanda ke yunkurin karya dokar. Ya ce, za a kafa wata runduna da za ta yi aiki.
Gwamnatin da Gwamna Wike ke jagoranta za ta zo karshe bayan babban zabe a 2023.