fidelitybank

Rikicin Ukraine: Amurka za ta mayar da martani kan Rasha – Biden

Date:

Fadar White House ta ce shugaban Amurka Joe Biden, ya shaidawa shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskiy cewa, Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine.

Wannan kiran dai ya zo ne kwanaki kadan bayan da Biden ya yi wata tattaunawa ta biyu a cikin wata guda da shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin, a cikin tashe-tashen hankula a kan iyakar Rasha da Ukraine, inda Rasha ta tara dakaru kusan 100,000.

“Shugaba Biden ya bayyana karara cewa, Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine,” in ji kakakin fadar White House Jen Psaki a wata sanarwa da ya fitar kamar yadda kamfanin dilancin labarai na Reuters.

Biden da Zelenskiy sun tattauna shirye-shiryen gudanar da jerin tarurrukan diflomasiyya masu zuwa a nan gaba, domin magance rikicin, a cewar fadar White House.

Zelenskiy ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter cewa, sun tattauna matakan hadin gwiwa kan wanzar da zaman lafiya a Turai da kuma hana ci gaba da ruruwa.

Wakilai daga Amurka da Rasha na shirin yin wata tattaunawa a tsakanin ranakun 9 zuwa 10 ga watan Janairu a birnin Geneva, sai kuma tattaunawar majalisar Rasha da NATO da kuma taron kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai.

Biden ya ce ya shaida wa Putin cewa ya na da muhimmanci Rashawa su dauki matakai domin sassauta rikicin kafin wadannan tarurrukan.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp