Fadar White House ta ce shugaban Amurka Joe Biden, ya shaidawa shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskiy cewa, Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine.
Wannan kiran dai ya zo ne kwanaki kadan bayan da Biden ya yi wata tattaunawa ta biyu a cikin wata guda da shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin, a cikin tashe-tashen hankula a kan iyakar Rasha da Ukraine, inda Rasha ta tara dakaru kusan 100,000.
“Shugaba Biden ya bayyana karara cewa, Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine,” in ji kakakin fadar White House Jen Psaki a wata sanarwa da ya fitar kamar yadda kamfanin dilancin labarai na Reuters.
Biden da Zelenskiy sun tattauna shirye-shiryen gudanar da jerin tarurrukan diflomasiyya masu zuwa a nan gaba, domin magance rikicin, a cewar fadar White House.
Zelenskiy ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter cewa, sun tattauna matakan hadin gwiwa kan wanzar da zaman lafiya a Turai da kuma hana ci gaba da ruruwa.
Wakilai daga Amurka da Rasha na shirin yin wata tattaunawa a tsakanin ranakun 9 zuwa 10 ga watan Janairu a birnin Geneva, sai kuma tattaunawar majalisar Rasha da NATO da kuma taron kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai.
Biden ya ce ya shaida wa Putin cewa ya na da muhimmanci Rashawa su dauki matakai domin sassauta rikicin kafin wadannan tarurrukan.