fidelitybank

Rikicin Ukraine: Amurka za ta mayar da martani kan Rasha – Biden

Date:

Fadar White House ta ce shugaban Amurka Joe Biden, ya shaidawa shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskiy cewa, Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine.

Wannan kiran dai ya zo ne kwanaki kadan bayan da Biden ya yi wata tattaunawa ta biyu a cikin wata guda da shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin, a cikin tashe-tashen hankula a kan iyakar Rasha da Ukraine, inda Rasha ta tara dakaru kusan 100,000.

“Shugaba Biden ya bayyana karara cewa, Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine,” in ji kakakin fadar White House Jen Psaki a wata sanarwa da ya fitar kamar yadda kamfanin dilancin labarai na Reuters.

Biden da Zelenskiy sun tattauna shirye-shiryen gudanar da jerin tarurrukan diflomasiyya masu zuwa a nan gaba, domin magance rikicin, a cewar fadar White House.

Zelenskiy ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter cewa, sun tattauna matakan hadin gwiwa kan wanzar da zaman lafiya a Turai da kuma hana ci gaba da ruruwa.

Wakilai daga Amurka da Rasha na shirin yin wata tattaunawa a tsakanin ranakun 9 zuwa 10 ga watan Janairu a birnin Geneva, sai kuma tattaunawar majalisar Rasha da NATO da kuma taron kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai.

Biden ya ce ya shaida wa Putin cewa ya na da muhimmanci Rashawa su dauki matakai domin sassauta rikicin kafin wadannan tarurrukan.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...
X whatsapp