fidelitybank

Rikicin Ukraine: Amurka za ta mayar da martani kan Rasha – Biden

Date:

Fadar White House ta ce shugaban Amurka Joe Biden, ya shaidawa shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelenskiy cewa, Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine.

Wannan kiran dai ya zo ne kwanaki kadan bayan da Biden ya yi wata tattaunawa ta biyu a cikin wata guda da shugaban kasar Rasha, Vladimir Putin, a cikin tashe-tashen hankula a kan iyakar Rasha da Ukraine, inda Rasha ta tara dakaru kusan 100,000.

“Shugaba Biden ya bayyana karara cewa, Amurka da kawayenta za su mayar da martani mai tsauri idan Rasha ta kara mamaye Ukraine,” in ji kakakin fadar White House Jen Psaki a wata sanarwa da ya fitar kamar yadda kamfanin dilancin labarai na Reuters.

Biden da Zelenskiy sun tattauna shirye-shiryen gudanar da jerin tarurrukan diflomasiyya masu zuwa a nan gaba, domin magance rikicin, a cewar fadar White House.

Zelenskiy ya bayyana hakan a shafinsa na Twitter cewa, sun tattauna matakan hadin gwiwa kan wanzar da zaman lafiya a Turai da kuma hana ci gaba da ruruwa.

Wakilai daga Amurka da Rasha na shirin yin wata tattaunawa a tsakanin ranakun 9 zuwa 10 ga watan Janairu a birnin Geneva, sai kuma tattaunawar majalisar Rasha da NATO da kuma taron kungiyar tsaro da hadin gwiwa a Turai.

Biden ya ce ya shaida wa Putin cewa ya na da muhimmanci Rashawa su dauki matakai domin sassauta rikicin kafin wadannan tarurrukan.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naÉ—in...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...
X whatsapp