fidelitybank

Janar Qasem: A gurfanar da Trump ko mu dauki fansa – Iran

Date:

Shugaban kasar Iran, Ibrahim Raisi ya lashi takobin daukar fansa a kan kisan da Amurka ta yi wa marigayi Janar Qasem Soleimani shekaru biyu da suka gabata, matukar ba a gurfanar da tsohon shugaban Amurka Donald Trump a gaban kotu ba.

Iran da kungiyoyin da ke kawance da ita a Iraki sun gudanar da bukukuwan girmama Soleimani, kwamandan dakarun Quds, reshen dakarun kare juyin juya hali na kasashen ketare.

An kashe Janar Qasem a Iraki a wani harin da jiragen yaki mara matuka suka kai ranar 3 ga Janairu, 2020, wanda shugaba Trump na lokacin ya ba da umarnin.

“Idan ba a gurfanar da Trump da (tsohon sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo a gaban kotu ba, to gaskiya kan laifin kisan Janar Soleimani za su dauki fansar shahadar mu,” in ji Raisi a wani jawabi da ya yi ta gidan talabijin a ranar Litinin.

A ranar Lahadin da ta gabata, Iran ta bukaci kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a cikin wata wasika da ya kama Amurka da Isra’ila, wadanda Tehran ta ce su ma suna da hannu a kisan, kamar yadda kafafen yada labaran Iran suka rawaito.

Kwanaki bayan kisan, Amurka ta shaidawa Majalisar Dinkin Duniya cewa kisan kare dangi ne, ta kuma sha alwashin daukar karin matakin “kamar yadda ya dace” a yankin Gabas ta Tsakiya, domin kare ma’aikatan Amurka da muradunta.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci Æ™arya ne – Ƴansanda

Rundunar Æ´ansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaÉ—awa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp