fidelitybank

Rikicin APC: Alhakina ne ci gaba da bunkasa Kano da ayyuka – Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya jaddada kudirinsa na ci gaba da bunkasa jihar duk kuwa da yunkurin da wasu ‘yan siyasa ke yi na kawo tsaiko a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a gidan gwamnatin jihar Kano, a ranar Lahadin da ta gabata, tare da halartar dukkan bangarorin masu ruwa da tsaki.

Ya ce, “Ya na da matukar muhimmanci kowa ya san cewa hazakarmu ta siyasa da gogewar siyasarmu ba za su bari rikicin kananan jam’iyya ya karkatar da hankalinmu wajen kara bunkasa jiharmu ta Kano ba. Abin da ke faruwa wani bangare ne na al’adar dimokuradiyya,” inji Ganduje yayin da ya ke mayar da martani kan rikicin jam’iyyar APC na Kano.

Sanata Kabiru Ibrahim Gaya da ‘yan majalisar wakilai 20, kakakin majalisar dokokin jihar Kano, da ‘yan majalisar dokokin jihar 28, da shugabannin kananan hukumomi 44, dukkan shugabannin jam’iyyar APC mai mulki daga mazabar 484 da kananan hukumomi 44 da kuma shugabannin jam’iyyar na jihar da dattawan jihar da dai sauran su, wadanda su ka halarci taron, sun kada kuri’ar amincewa da gwamnan.

A cewar sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran gwamnan jihar, Anwar Abba, wanda PlatinumPost ta samu a ranar Lahadin da ta gabata, Ganduje yayin da ya ke tunatar da masu ruwa da tsaki a kan tsarin da a ka bi a taron gundumomi da na kananan hukumomi na jam’iyyar, ta ce dukkanin hanyoyin sun bi ka’idoji.

A kan shirin da wasu ‘yan siyasa ke yi na kawo ruguza sha’anin mulki a jihar, Ganduje ya ce shi ba sabon salo ba ne a irin wannan salon siyasar.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp