fidelitybank

Rikicin APC: Alhakina ne ci gaba da bunkasa Kano da ayyuka – Ganduje

Date:

Gwamnan jihar Kano, Dr. Abdullahi Ganduje, ya jaddada kudirinsa na ci gaba da bunkasa jihar duk kuwa da yunkurin da wasu ‘yan siyasa ke yi na kawo tsaiko a jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a yayin wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a gidan gwamnatin jihar Kano, a ranar Lahadin da ta gabata, tare da halartar dukkan bangarorin masu ruwa da tsaki.

Ya ce, “Ya na da matukar muhimmanci kowa ya san cewa hazakarmu ta siyasa da gogewar siyasarmu ba za su bari rikicin kananan jam’iyya ya karkatar da hankalinmu wajen kara bunkasa jiharmu ta Kano ba. Abin da ke faruwa wani bangare ne na al’adar dimokuradiyya,” inji Ganduje yayin da ya ke mayar da martani kan rikicin jam’iyyar APC na Kano.

Sanata Kabiru Ibrahim Gaya da ‘yan majalisar wakilai 20, kakakin majalisar dokokin jihar Kano, da ‘yan majalisar dokokin jihar 28, da shugabannin kananan hukumomi 44, dukkan shugabannin jam’iyyar APC mai mulki daga mazabar 484 da kananan hukumomi 44 da kuma shugabannin jam’iyyar na jihar da dattawan jihar da dai sauran su, wadanda su ka halarci taron, sun kada kuri’ar amincewa da gwamnan.

A cewar sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labaran gwamnan jihar, Anwar Abba, wanda PlatinumPost ta samu a ranar Lahadin da ta gabata, Ganduje yayin da ya ke tunatar da masu ruwa da tsaki a kan tsarin da a ka bi a taron gundumomi da na kananan hukumomi na jam’iyyar, ta ce dukkanin hanyoyin sun bi ka’idoji.

A kan shirin da wasu ‘yan siyasa ke yi na kawo ruguza sha’anin mulki a jihar, Ganduje ya ce shi ba sabon salo ba ne a irin wannan salon siyasar.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp