fidelitybank

Ranar 17 ga watan Maris za a fara sauraron daukaka karar Inusa Yellow

Date:

Kotun daukaka kara da ke garin Fatakwal ta sanya ranar 17 ga watan Maris, domin fara sauraron karar da Yunusa Yellow ya daukaka a gabanta na kalubalantar hukuncin babbar kotun jihar Bayelsa.

Lauyoyin Yunusa Yellow, Sunusi Musa ne ya sanar da hakan a shafinsa na Facebook ranar Talata.

Sauran lauyiyon da za su tsayawa Yunusa Yellow sun hadar da Huwaila Muhammad da Abdul Muhammad Rafindadi, da kuma Kayode Olasebikan.

Idan za a iya tunawa tun a shekarar 2015 ne aka kama Yunusa Yellow bisa zargin sato wata yarinya Ese Oruru da ga jihar Bayelsa zuwa Kano.

Yunusa Yellow dai ya taho da yarinyar Ese ne zuwa Kano suka kuma yi aure, sai dai an kama shi da laifin satar mutane da kuma safarar kananan yara.

Bayan kama shi ne a nan Kano aka kuma aike da shi can jihar Bayelsa garin da yarinyar ta ke domin a yanke masa hukunci.

Babbar kotun jihar dai ta zargeshi da laifuka har guda biyar da suka hadar da garkuwa da mutane da hakkewa karamar yarinya, da kuma yin amfani da dama kan karamar yariwa, sai kuma laifin yin amafani da karancin shekarunta wajen yi mata wayo. Saboda hakan ne kotun ta yanke masa hukuncin daurin shekaru 26 a gidan yari a can Bayelsa.

Sai dai da yake yanke hukunci alkalin kotun, Jane Inyanga, ta ce, Yunusa bai aikata laifi na farko ba wato garkuwa da mutane.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp