fidelitybank

Ranar 17 ga watan Maris za a fara sauraron daukaka karar Inusa Yellow

Date:

Kotun daukaka kara da ke garin Fatakwal ta sanya ranar 17 ga watan Maris, domin fara sauraron karar da Yunusa Yellow ya daukaka a gabanta na kalubalantar hukuncin babbar kotun jihar Bayelsa.

Lauyoyin Yunusa Yellow, Sunusi Musa ne ya sanar da hakan a shafinsa na Facebook ranar Talata.

Sauran lauyiyon da za su tsayawa Yunusa Yellow sun hadar da Huwaila Muhammad da Abdul Muhammad Rafindadi, da kuma Kayode Olasebikan.

Idan za a iya tunawa tun a shekarar 2015 ne aka kama Yunusa Yellow bisa zargin sato wata yarinya Ese Oruru da ga jihar Bayelsa zuwa Kano.

Yunusa Yellow dai ya taho da yarinyar Ese ne zuwa Kano suka kuma yi aure, sai dai an kama shi da laifin satar mutane da kuma safarar kananan yara.

Bayan kama shi ne a nan Kano aka kuma aike da shi can jihar Bayelsa garin da yarinyar ta ke domin a yanke masa hukunci.

Babbar kotun jihar dai ta zargeshi da laifuka har guda biyar da suka hadar da garkuwa da mutane da hakkewa karamar yarinya, da kuma yin amfani da dama kan karamar yariwa, sai kuma laifin yin amafani da karancin shekarunta wajen yi mata wayo. Saboda hakan ne kotun ta yanke masa hukuncin daurin shekaru 26 a gidan yari a can Bayelsa.

Sai dai da yake yanke hukunci alkalin kotun, Jane Inyanga, ta ce, Yunusa bai aikata laifi na farko ba wato garkuwa da mutane.

punch newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp