fidelitybank

Rana ta 11: Sojoji sun harbe masu zanga-zanga a Sudan

Date:

Jami’an tsaron kasar Sudan sun harbe mutane hudu a wani samame da a ka yi a fadin kasar a kan zanga-zangar adawa da mulkin soja a ranar 30 ga watan Disamba, kamar yadda ‘yan sandan Sudan suka sanar a ranar Juma’a.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, jami’an tsaro sun harba barkonon tsohuwa da gurneti a yayin da masu zanga-zangar suka bi ta birnin Khartoum da garuruwan Omdurman da Bahri dake makwabtaka da fadar shugaban kasa a jiya Alhamis.

A wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar sun ce an kashe mutane hudu a Omdurman, sannan masu zanga-zangar 297 da jami’an ‘yan sanda 49 sun jikkata a fadin kasar a zanga-zangar da ta hada dubun dubatar mutane.

Tashar talabijin ta Al Hadath ta rawaito cewa, mai ba da shawara ga shugaban soji, Abdel Fattah Al-Burhan na cewa, sojoji ba za su bari kowa ya jawo kasar cikin rudani ba, kuma ci gaba da zanga-zangar ta kasance kumfar baki ne, domin haka “ba za su bari kowa ya jefa kasar cikin rudani ba. domin cimma mafita ta siyasa.

Zanga-zangar ta ranar Alhamis ta kasance zagaye na rana 11 na manyan zanga-zangar, tun bayan juyin mulkin ranar 25 ga watan Oktoba da ya sa a ka tsige, Abdallah Hamdok, sannan kuma a ka mayar da shi kan karagar mulki. Sai dai masu zanga-zangar dai sun bukaci sojoji da kada su taka rawar gani a cikin gwamnati a lokacin mika mulki a yayin zabe.

Gamayyar Kungiyoyin ‘Yanci da Sauyi ta ce, jami’an tsaro “Sun yi amfani da danniya fiye da kima” a ranar Alhamis tare da yin kira ga al’ummomin yankuna da na kasa da kasa da kungiyoyin kare hakkin bil’adama da su yi Allah wadai da juyin mulkin.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Ę“an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe Ę“an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aʙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ʙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ʙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaʙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp