fidelitybank

Rana ta 11: Sojoji sun harbe masu zanga-zanga a Sudan

Date:

Jami’an tsaron kasar Sudan sun harbe mutane hudu a wani samame da a ka yi a fadin kasar a kan zanga-zangar adawa da mulkin soja a ranar 30 ga watan Disamba, kamar yadda ‘yan sandan Sudan suka sanar a ranar Juma’a.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa, jami’an tsaro sun harba barkonon tsohuwa da gurneti a yayin da masu zanga-zangar suka bi ta birnin Khartoum da garuruwan Omdurman da Bahri dake makwabtaka da fadar shugaban kasa a jiya Alhamis.

A wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar sun ce an kashe mutane hudu a Omdurman, sannan masu zanga-zangar 297 da jami’an ‘yan sanda 49 sun jikkata a fadin kasar a zanga-zangar da ta hada dubun dubatar mutane.

Tashar talabijin ta Al Hadath ta rawaito cewa, mai ba da shawara ga shugaban soji, Abdel Fattah Al-Burhan na cewa, sojoji ba za su bari kowa ya jawo kasar cikin rudani ba, kuma ci gaba da zanga-zangar ta kasance kumfar baki ne, domin haka “ba za su bari kowa ya jefa kasar cikin rudani ba. domin cimma mafita ta siyasa.

Zanga-zangar ta ranar Alhamis ta kasance zagaye na rana 11 na manyan zanga-zangar, tun bayan juyin mulkin ranar 25 ga watan Oktoba da ya sa a ka tsige, Abdallah Hamdok, sannan kuma a ka mayar da shi kan karagar mulki. Sai dai masu zanga-zangar dai sun bukaci sojoji da kada su taka rawar gani a cikin gwamnati a lokacin mika mulki a yayin zabe.

Gamayyar Kungiyoyin ‘Yanci da Sauyi ta ce, jami’an tsaro “Sun yi amfani da danniya fiye da kima” a ranar Alhamis tare da yin kira ga al’ummomin yankuna da na kasa da kasa da kungiyoyin kare hakkin bil’adama da su yi Allah wadai da juyin mulkin.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp