Kungiyar malaman jami’o’i ta jihar Filato (PLASU) Bokkos, reshen kungiyar malaman jami’o’I ta kasa (ASUU) ta fara yajin aikin sai baba-ta-gani, domin matsawa bukatunta na inganta walwala da muhallin aiki.
Dr. Hassan Zitta da sakatare Deme Bitrus sun ce an cimma matsayar ayyana yajin aikin ne a taron ASUU da a ka gudanar a ranar Litinin, 20 ga watan Disamba.
A cewarsu, gwamnatin Filato ta gaza mutunta yarjejeniyar da ta kulla da kungiyar, domin haka ne a ka yanke shawarar daukar matakin.
Kungiyar a cikin sanarwar da ta fitar ta ce, matsalar da a ke fama da ita ta na da nasaba da karuwar rashin tsaro a jami’ar da kuma rashin biyan kudaden alawus-alawus.
Dalilan, kungiyar ta ce akwai karancin masauki ga dalibai da ma’aikata da kuma bukatar gwamnati ta kara gina dakunan karatu da dai sauransu.