Matakin shugaba Buhari na ƙin sanya hannu kan kuɗirin dokar zaɓe da majalisar dokoki ta amince na ci gaba da haifar da ce-ce-ku-ce a Najeriya.
Batun zaɓen ƴar tinke ya fi jan hankali a kuɗirin doka, kuma Shugaban ya bayyana dalilansa na ƙin sanya hannu, a wasiƙar da ya rubutawa majalisa, inda ya ce zaben ‘yar tinke zai lakume kuɗi da kuma bayyana fargabar ƙalubalen tsaro wurin gudanar da shi.
Sai dai wannan matakin ya haifar da mahawara a shafukan sada zumunta inda wasu ke goyon bayan shugaban, wasu ƴan ƙasar da ƙungiyoyin fararen hula kuma ke sukar matakin tare da yin kira ga majalisa ta yi gaban kanta ta amince da kuɗirin ko da shugaban ya ƙi sa hannu.
Tuni Majalisar dokokin kasar ta amince da dokar da ta ƙunshi amincewa da batun zaɓen fid da gwani ta hanyar ƴar tinƙe wanda aka fi sani da ƙato bayan ƙato.
Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari kawai a ke jira ya sanya hannu a kuɗirin, domin ya zama doka, kuma yanzu ya ƙi sanya hannu. A cewar BBC.