fidelitybank

Philipine: Shugaba Duterte ya rattaba hannu kan kasafi Pesos tiriliyan 5.024

Date:

Shugaban kasar Philippine, Rodrigo Duterte, ya rattaba hannu kan kasafin kudinshin kudi nan a pesos tiriliyan 5.024 kwatankacin (dala biliyan 98.45) na shekara mai zuwa, kasa mafi girma a kudu maso gabashin Asiya, da nufin ci gaba da farfado da tattalin arziki da sarrafa barkewar COVID-19.

Kasafin kudin kasar, wanda ya fi na shirin kashe kudi na bana da kashi 11.5, shi ne na karshe na gwamnatin Duterte, kafin wa’adin mulkin sa na shekara shida ya kare a watan Yuni.

“Kasafin kudin shekarar 2022 zai zama kwarin gwiwa kan ayyukan da su ka mai da hankali kan samar da juriya a cikin halin, da ci gaba da samun murmurewa a fannin tattalin arziki, da ci gaba da samar da ababen more rayuwa,” Inji ofishin Duterte a cikin wata sanarwa.

Ya hada da fitar da babban kudi na peso tiriliyan 1, doMIn kashe kayayyakin more rayuwa, tallafin kasafin kudi ga kamfanonin jiha, da mika babban birnin ga kananan hukumomi.

Philippines, ta kasance daga cikin kasashen da annobar COVID-19 ta fi kamari a Asiya, ta na shirin kashe kusan pesos biliyan 48.2 domin siyan rigakafin cutar a shekara mai zuwa yayin da ta ke haɓaka shirinta na haɓakawa.

Kasar ta ware peso biliyan 23 domin gina sabbin cibiyoyin kiwon lafiya da fadadawa da inganta wadanda a ke da su, da kuma sayo kayayyakin aiki ga asibitoci.

Haka kuma gwamnati za ta kashe peso miliyan 983 domin kafa cibiyar kula da cutar, wanda zai taimaka wa gwamnati wajen yin nazari da magance sabbin kwayoyin cuta, masu tasowa, da masu sake bullowa.

 

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp