fidelitybank

PDP ta jinjina wa sojojin Najeriya a fagen daga

Date:

Jam’iyyar hamayya ta PDP, ta jinjina wa sojojin Najeriya, bisa jajircewa da sadaukar da kai da su ke yi a ƙasar nan, musamman a lokacin da ta fuskanci tabarbarewar tsaro a cikin shekaru shida da suka gabata.

Jam’iyyar PDP ta yi na’am da irin bajinta da kishin kasa da jiga-jigan sojojin ke yi a fagen daga, wadanda duk da kalubalen da ake fuskanta a kullum, suna jefa rayuwarsu cikin kangi, inda da yawa suke rasa rayukan su, domin hadin kai da tsaron Najeriya.

PDP ta bayyana hakan ne a lokaci bikin tunawa da ƴan mazan jiya wanda aka gudanar a ranar Asabar.

Jam’iyyar PDP, ta kuma bukaci gwamnati ta dauki matakin samarwa sojojin isassun kayan aiki tare da inganta jin dadin sojojin, domin tabbatar da ingancin aikinsu ga ƙasa.

Ta ce, “Jam’iyyar mu kira ga gwamnati da ta tabbatar da jin dadin iyalan jaruman mu wadanda suka sadaukar da rayukansu, domin al’ummarmu. Kar a bar iyalansu da ‘yan uwansu su ci gaba da shan wahala”. A cewar PDP.

Jam’iyyar PDP ta kuma bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da bayar da goyon baya da kuma yi wa sojoji addu’a a babban aikinsu na kare ƴan Najeriya.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaƙi da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunƙasa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban ƙasa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp