Jam’iyyar hamayya ta PDP, ta jinjina wa sojojin Najeriya, bisa jajircewa da sadaukar da kai da su ke yi a ƙasar nan, musamman a lokacin da ta fuskanci tabarbarewar tsaro a cikin shekaru shida da suka gabata.
Jam’iyyar PDP ta yi na’am da irin bajinta da kishin kasa da jiga-jigan sojojin ke yi a fagen daga, wadanda duk da kalubalen da ake fuskanta a kullum, suna jefa rayuwarsu cikin kangi, inda da yawa suke rasa rayukan su, domin hadin kai da tsaron Najeriya.
PDP ta bayyana hakan ne a lokaci bikin tunawa da ƴan mazan jiya wanda aka gudanar a ranar Asabar.
Jam’iyyar PDP, ta kuma bukaci gwamnati ta dauki matakin samarwa sojojin isassun kayan aiki tare da inganta jin dadin sojojin, domin tabbatar da ingancin aikinsu ga ƙasa.
Ta ce, “Jam’iyyar mu kira ga gwamnati da ta tabbatar da jin dadin iyalan jaruman mu wadanda suka sadaukar da rayukansu, domin al’ummarmu. Kar a bar iyalansu da ‘yan uwansu su ci gaba da shan wahala”. A cewar PDP.
Jam’iyyar PDP ta kuma bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da bayar da goyon baya da kuma yi wa sojoji addu’a a babban aikinsu na kare ƴan Najeriya.