fidelitybank

PDP ta jinjina wa sojojin Najeriya a fagen daga

Date:

Jam’iyyar hamayya ta PDP, ta jinjina wa sojojin Najeriya, bisa jajircewa da sadaukar da kai da su ke yi a ƙasar nan, musamman a lokacin da ta fuskanci tabarbarewar tsaro a cikin shekaru shida da suka gabata.

Jam’iyyar PDP ta yi na’am da irin bajinta da kishin kasa da jiga-jigan sojojin ke yi a fagen daga, wadanda duk da kalubalen da ake fuskanta a kullum, suna jefa rayuwarsu cikin kangi, inda da yawa suke rasa rayukan su, domin hadin kai da tsaron Najeriya.

PDP ta bayyana hakan ne a lokaci bikin tunawa da ƴan mazan jiya wanda aka gudanar a ranar Asabar.

Jam’iyyar PDP, ta kuma bukaci gwamnati ta dauki matakin samarwa sojojin isassun kayan aiki tare da inganta jin dadin sojojin, domin tabbatar da ingancin aikinsu ga ƙasa.

Ta ce, “Jam’iyyar mu kira ga gwamnati da ta tabbatar da jin dadin iyalan jaruman mu wadanda suka sadaukar da rayukansu, domin al’ummarmu. Kar a bar iyalansu da ‘yan uwansu su ci gaba da shan wahala”. A cewar PDP.

Jam’iyyar PDP ta kuma bukaci ‘yan Najeriya da su ci gaba da bayar da goyon baya da kuma yi wa sojoji addu’a a babban aikinsu na kare ƴan Najeriya.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp