Shugaban majalisar dattawa ta kasa, Sanata Ahmad Lawan, ya yabawa Kibiyan Kebbi kuma bulaliyar majalisa, Sanata Orji Uzo Kalu, bisa irin gudunmawar da ya ke baiwa majalisa dama kasa baki daya.
Sanatan Ahmad Lawan ya bayyana Kibiyan Kebbi, Orji Uzo Kalu a matsayin mutum mai kishin al’umma, sakamakon gudunmawar da ya ke baiwa ‘yan kasa.
Sanarwar mai kunshe da sa hanun mai taimaka masa a harkokin Arewa, Aminu Shehu Uba Sharada, a yayin da Orji Uzo Kalu ke mika sakon ta’aziyar sa ga daukacin al’ummar muslmai da jihar Sokoto na kona mutane da ‘yan ta’adda su ka yi.
Ya ce,”Kibiyan Kebbi, mutum ne dan yankin Kudu maso Gabas, amma ya fi karfi a Arewacin kasar nan, ni na rasa yadda zan bayyana shi, saboda gudunmawar da ya ke bayarwa wajen hada kan ‘yan kasa da gina al’umma.
Ya kuma ce”Amma gaskiya wannan ya nuna cewa mutum ne mai kishin Najeriya, na zauna daki daya da shi a jami’ar Maiduguri a shekarar 1980, a matsayin dalibai, na san ba zai baiwa ‘yan Najeriya kunya ba, wajen hada kan ‘yan kasa, mutum ne kuma mai yi wa kasa addu’a na samun zaman lafiya a zama wuri guda, kuma dama mu addu’ar mu kenan wajen zama Najeriya dunkulalliya, mu aikin mu shugabanni shi ne, mu wakilai ne na hada kan kasa da al’umma, kuma kamar yadda mu ke ‘yan majalisu a yanzu shi ne Najeriyar ce a gaban mu, mun yarda cewa Najeriya daya ce, kuma za mu sa Najeriya a gaba, saboda al’umma mu ke yi wa aiki, kuma dukannin mu mun fito daga mazabun mu”. Inji Sanata Ahmad Lawan.