fidelitybank

Orji Uzo Kalu mutum ne mai son ci gaban kasa da kishin al’umma – Ahamd Lawan

Date:

Shugaban majalisar dattawa ta kasa, Sanata Ahmad Lawan, ya yabawa Kibiyan Kebbi kuma bulaliyar majalisa, Sanata Orji Uzo Kalu, bisa irin gudunmawar da ya ke baiwa majalisa dama kasa baki daya.

Sanatan Ahmad Lawan ya bayyana Kibiyan Kebbi, Orji Uzo Kalu a matsayin mutum mai kishin al’umma, sakamakon gudunmawar da ya ke baiwa ‘yan kasa.

Sanarwar mai kunshe da sa hanun mai taimaka masa a harkokin Arewa, Aminu Shehu Uba Sharada, a yayin da Orji Uzo Kalu ke mika sakon ta’aziyar sa ga daukacin al’ummar muslmai da jihar Sokoto na kona mutane da ‘yan ta’adda su ka yi.

Ya ce,”Kibiyan Kebbi, mutum ne dan yankin Kudu maso Gabas, amma ya fi karfi a Arewacin kasar nan, ni na rasa yadda zan bayyana shi, saboda gudunmawar da ya ke bayarwa wajen hada kan ‘yan kasa da gina al’umma.

Ya kuma ce”Amma gaskiya wannan ya nuna cewa mutum ne mai kishin Najeriya, na zauna daki daya da shi a jami’ar Maiduguri a shekarar 1980, a matsayin dalibai, na san ba zai baiwa ‘yan Najeriya kunya ba, wajen hada kan ‘yan kasa, mutum ne kuma mai yi wa kasa addu’a na samun zaman lafiya a zama wuri guda, kuma dama mu addu’ar mu kenan wajen zama Najeriya dunkulalliya, mu aikin mu shugabanni shi ne, mu wakilai ne na hada kan kasa da al’umma, kuma kamar yadda mu ke ‘yan majalisu a yanzu shi ne Najeriyar ce a gaban mu, mun yarda cewa Najeriya daya ce, kuma za mu sa Najeriya a gaba, saboda al’umma mu ke yi wa aiki, kuma dukannin mu mun fito daga mazabun mu”. Inji Sanata Ahmad Lawan.

 

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp