Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI) ta yi kira ga al’ummar musulmai a Najeriya da su dukufa da yin addu’o’i ta musamman, domin neman dauki daga Allah a bangaren tsaron da a ke fama da ita a Najeriya.
Sanarwa mai kunshe da sa hannun Babban Sakataren kungiyar, Dr Khalid Aliyu ya fitar ranar Lahadi, a ka kuma rabawa manema labarai ta ce, addu’a ita ce hanya daya da za a iya bi a yanzu, wajen neman dauki daga wurin Ubangiji.
Sanarwar ta kuma ce, duk halin da a ka shiga na kunci ko wani abun, a mika lamarin zuwa wajen Ubangiji, domin shi ne mafita ga komai.
“Ba bu abun da ya gagar, kuma baa bun da ya fi karfin Allah madaukakin Sarki, domin kuwa shi ne mai rahama mai jinkai”. Inji Dr Khalid.
Wannan na zuwa ne adaidai lokacin da kasar nan ke fuskantar yawaitar ta’addanci da ya yi kamari a wasu sassan jihohin kasar nan ciki harda yankin Arewa.