Bulalaiyar majalisar dattawa kuma dan takarar shugaban kasa a 2023, Sanata Orji Uzor Kalu a daren ranar Talata ya kai wa shugaban kasa Muhammadu Buhari ziyara.
Da ya ke sanar da ziyarar a shafin sa na Facebook da aka tabbatar, kalu ya rubuta cewa, “A daren yau, na kai wa shugaban kasa Muhammadu Buhari ziyara domin tattaunawa kan manyan al’amuran kasa, kuma na gamsu da tattaunawar da muka yi, na bar shi da karfe 10 na dare kuma cikin koshin lafiya, muna sa ran Najeriya ta ci gaba wajen kai wa ga gaci.”

Ziyarar Orji Kalu na da nasaba da neman ganin ya samu damar dare kujerar shugaban kasa a shekarar 2023.