fidelitybank

Omicron:  Mutum 45 sun kamu da cutar a Najeriya – NCDC

Date:

A jiya ne Cibiyar Kula da Cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta sanar da cewa kawo yanzu an samu bullar cutar guda 45 na Omicron na COVID-19 a kasar nan, ba tare da an samu mace-mace ba.

Darakta-Janar na NCDC, Dr Ifedayo Adetifa, wanda ya bayyana kididdigar Omicron ta Najeriya a wani taron manema labarai, ya ce, sabbin kwayoyin cutar sun kasance a cikin mutanen da ba su da tarihin tafiya, wanda ke nuna cewa kasar ta riga ta fara kamuwa da cutar.

Adetifa ya ce”Mutane Shida na Omicron da a ka gano a baya su na cikin mutanen da ke da tarihin balaguro zuwa Afirka ta Kudu, ya na da kyau ‘yan Najeriya su kiyaye tazarar jiki tare da kaucewa cudanya da duk wanda ke nuna alamun cutar numfashi”.

Ya kara da cewa “Muna dogaro da ku kare kanku da masoyinka daga COVID-19,” inji shi.

Adetifa ya kuma shawarci ‘yan Najeriya da su kara bin matakan da za su iya dakile yaduwar Omicron kamar su rage yawan taro, kara nisantar jiki, tsawon lokacin saduwa da kuma yiwuwar rufe wuraren da a ke ganin suna da hadari sosai.

Adetifa ya bukaci ‘yan Najeriya da su dauki shawarar da kwamitin shugaban kasa ya bayar kan COVID-19 da muhimmanci, ya kara da cewa hakan zai kara habaka tasirin irin wadannan ayyukan.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp