Kungiyar kwadago ta kasa NLC reshen jihar Kano, ta bayyana kaduwarta dangane da rasuwar mashahuran mutane ‘yan kishin kasa ‘yan asalin jihar Kano a baya bayan nan.
Ta cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar mai dauke sa hannun shugaban kungiyar, NLC a Kano, Kwamared Kabiru Ado Munjibir.
NLC ta ce,”Al’umma a Kano ba za su taba manta irin gudunmawar da Alhaji Bashir Othman Tofa da Marigayi Ado Gwaram da kuma Inuwa Musa Kwankwaso su ka baiwa jihar Kano ba ta kowacce fuska, domin ciyar da jihar gaba a lokacin da su ke raye.
Kungiyar ta kuma mika sakon ta’aziyyarta ga iyalai da ‘yan uwan mamatan dama sauran al’ummar jihar Kano, saboda gagarumin rashin da a ka yi na wadannan fitattun mutane ‘yan kishin kasa.
Sanarwar ta kuma taya ma’aikatan jihar Kano murnar shiga sabuwar shekarar 2022, ta kuma yi fatan samun dorewar zaman lafia a shekarar da muka shiga ta 2022.