fidelitybank

NLC: Buhari ya fuskanci gagarumin zanga-zanga a 2022

Date:

Kungiyar Kwadago NLC ta gargadi shugaban kasa, Muhammadu Buhari game da shirin cire tallafin man fetur a shekarar 2022, inda ta ce matakin zai fuskanci gagarumar zanga-zanga a fadin kasar.

Kungiyar ta ce za a fara gudanar da gangamin ne ba tare da gargadi ba, idan har gwamnatin tarayya ta sanar da sabon farashin man fetur gabanin gudanar da zanga-zangar da za a yi a dukkan jihohin kasar nan.

An shirya gudanar da zanga-zangar ne a ranar 27 ga watan Janairu, 2022, kuma za ta kai ga mika wa dukkan gwamnonin jihohi 36 wasikun zanga-zangar.

Bayan haka, NLC ta ce, za a kuma gudanar da zanga-zangar kasa a Abuja a ranar 1 ga Fabrairu.

Wadannan na daga cikin kudurorin majalisar zartarwa ta kasa na kungiyar NLC da aka gudanar a gidan ma’aikata dake Abuja a ranar Juma’a.

Gwamnatin tarayya ta ce, za ta cire tallafin man fetur a shekara mai zuwa biyo bayan shawarar da asusun lamuni na duniya da bankin duniya suka bayar.

A nata bangaren, ministar kudi, Misis Zainab Ahmed, ta ce, kimanin talakawan Najeriya miliyan 40 ne za a rika biyansu alawus din sufuri na Naira 5,000 duk wata.

 

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp