fidelitybank

NLC: Buhari ya fuskanci gagarumin zanga-zanga a 2022

Date:

Kungiyar Kwadago NLC ta gargadi shugaban kasa, Muhammadu Buhari game da shirin cire tallafin man fetur a shekarar 2022, inda ta ce matakin zai fuskanci gagarumar zanga-zanga a fadin kasar.

Kungiyar ta ce za a fara gudanar da gangamin ne ba tare da gargadi ba, idan har gwamnatin tarayya ta sanar da sabon farashin man fetur gabanin gudanar da zanga-zangar da za a yi a dukkan jihohin kasar nan.

An shirya gudanar da zanga-zangar ne a ranar 27 ga watan Janairu, 2022, kuma za ta kai ga mika wa dukkan gwamnonin jihohi 36 wasikun zanga-zangar.

Bayan haka, NLC ta ce, za a kuma gudanar da zanga-zangar kasa a Abuja a ranar 1 ga Fabrairu.

Wadannan na daga cikin kudurorin majalisar zartarwa ta kasa na kungiyar NLC da aka gudanar a gidan ma’aikata dake Abuja a ranar Juma’a.

Gwamnatin tarayya ta ce, za ta cire tallafin man fetur a shekara mai zuwa biyo bayan shawarar da asusun lamuni na duniya da bankin duniya suka bayar.

A nata bangaren, ministar kudi, Misis Zainab Ahmed, ta ce, kimanin talakawan Najeriya miliyan 40 ne za a rika biyansu alawus din sufuri na Naira 5,000 duk wata.

 

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp