Kungiyar Kwadago NLC ta gargadi shugaban kasa, Muhammadu Buhari game da shirin cire tallafin man fetur a shekarar 2022, inda ta ce matakin zai fuskanci gagarumar zanga-zanga a fadin kasar.
Kungiyar ta ce za a fara gudanar da gangamin ne ba tare da gargadi ba, idan har gwamnatin tarayya ta sanar da sabon farashin man fetur gabanin gudanar da zanga-zangar da za a yi a dukkan jihohin kasar nan.
An shirya gudanar da zanga-zangar ne a ranar 27 ga watan Janairu, 2022, kuma za ta kai ga mika wa dukkan gwamnonin jihohi 36 wasikun zanga-zangar.
Bayan haka, NLC ta ce, za a kuma gudanar da zanga-zangar kasa a Abuja a ranar 1 ga Fabrairu.
Wadannan na daga cikin kudurorin majalisar zartarwa ta kasa na kungiyar NLC da aka gudanar a gidan ma’aikata dake Abuja a ranar Juma’a.
Gwamnatin tarayya ta ce, za ta cire tallafin man fetur a shekara mai zuwa biyo bayan shawarar da asusun lamuni na duniya da bankin duniya suka bayar.
A nata bangaren, ministar kudi, Misis Zainab Ahmed, ta ce, kimanin talakawan Najeriya miliyan 40 ne za a rika biyansu alawus din sufuri na Naira 5,000 duk wata.