Hukumar shirya jarabawa ta kasa (NECO) ta ce ta fara wani yunkuri na ganin cewa jarrabawar ta zama tilas a dukkan jihohin kasar nan.
A cikin wata sanarwa da ta fito daga hannun shugabanta na yada labarai da hulda da jama’a, Mista Azeez Sani, ta bayyana fatan sauran jihohi za su bi bayan gwamnatin Cross River da ta amince da duk wani jarrabawar da NECO ta gudanar ya zama tilas ga dukkan makarantun gwamnati a jihar.
Sani ya ce,”Gwamnan Jihar Cross River, Farfesa Ben Ayade, ya amince da hakan ne biyo bayan bukatar da magatakardar hukumar ta NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya yi a wata ziyarar ban girma da ya kai wa Gwamnan a Calabar”.
Majalisar ta na gudanar da jarrabawar gama gari ta kasa (NCEE) da jarrabawar shaidar kammala karatun boko (BECE) da kuma babbar makarantar sakandare (SSCE).