Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA ta lalata magungunan da suka kai sama da Naira Biliyan 50 masu nauyin kilogiram 20,000.
Shugaban Hukumar NDLEA, Mai ritaya Birgediya Janar Buba Marwa ne ya bayyana haka ne a lokacin da ake kona haramtattun kwayoyi a bainar jama’a a Abuja.
Ya ce hukumar na fuskantar samun koma baya, kuma a yanzu haka a na ci gaba da yi mata aiki gadan-gadan.
Marwa, wanda Sakataren hukumar, Barista Shadrach Haruna, ya wakilta, ya ce girman magungunan da aka lalata, ya nuna irin girman matsalar shan miyagun kwayoyi da ake fuskanta a kasar nan.
A kwanakin baya ne dai shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da yaki a kan shan miyagun kwayoyi (WADA) na hukumar NDLEA a ranar 26 ga watan Yuni.