Gwamnan jihar Ebonyi, Cif David Nweze, ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Kano bisa rasuwar tsohon dan takarar shugaban kasa, Alhaji Bashir Othman Tofa.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun gwamnan, wanda a ka rabawa manema labarai.
Umahi ya ce; “Mun kadu kwarai da juyayi, bisa samun rasuwar tsohon dan takarar shugaban kasa na rusasshiyar jam’iyyar (NRC) Bashir Othman Tofa wanda abin bakin ciki ya faru a ranar 3 ga Janairu, 2022 ya na da shekaru 74 a duniya.
“Marigayi Tofa dan siyasa ne mai sassaucin ra’ayi kuma falsafar siyasa wanda tunanin siyasa da burinsa shine, samun kasa mai zaman lafiya, daidaito da adalci. Ya kasance ƙwararren masanin masana’antu wanda ya saka jari ba tare da son kai ba ga ɗan adam.
“Mun yi asara mutum kuma kyautatawar zuciyarsa. Muna addu’ar Allah ya jikansa da rahama ya baiwa iyalansa hakurin jure rashin da ba za a iya misalta shi ba.
“Domin haka muna mika wa iyalan mamacin, gwamnati da al’ummar Jihar Kano, addu’o’i da jin kai na gwamnati da al’ummar Jihar Ebonyi a wannan lokaci na bakin ciki.” A cewar Cif David Nweze.