Hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya (FAAN) ta kama mutane 90 a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke jihar Legas da kuma filin jirgin Nnamdi Azikwe da ke Abuja.
A wata sanarwa da Henrietta Yakubu, Babbar manaja a hukumar, ta bayyana ta bayyana su a matsayin masu aikata munanan ayyuka.
Ta ce, “Sumamen wani bangare ne na kokarin kawar da filayen saukar jiragen sama na kasar daga halin ke ciki. An dai kama wadanda a ke zargin saboda sakamakon gwaji na COVID-19 na karya, yawon bude ido, shiga ba tare da izini ba, cin zarafi, saukakawa ba bisa ka’ida ba, jabu, sata, da kuma damun jama’a”.
“Daga cikin wadanda a ka kama, 59 an mika su ga rundunar ‘yan sandan filin jirgin sama da ke Abuja, domin gurfanar da su gaban kuliya, yayin da 30 kuma a ka mika su ga ‘yan sanda a Legas,” in ji Yakubu.
FAAN ta gargadi wadanda ba su da halaltattun sana’o’i a tashoshin jiragen sama da ma’aikatan da ke gudanar da ayyukan ba bisa ka’ida ba da su daina.