Mambobin kungiyar ma’aikatan majalisar dokokin Najeriya (PASAN) sun gudanar da zanga-zanga a harabar majalisar dokokin kasar kan rashin biyansu kudaden alawus-alawus.
Ma’aikatan sun mamaye harabar ta NASS ne a safiyar ranar Litinin, inda suke rera wakokin hadin kai tare da nuna alluna daban-daban.
Daga cikin wasu bukatu, ma’aikatan na son a tabbatar da cikakken aiwatar da mafi karancin albashin ma’aikata na kasa a shekarar 2019 da kuma sake duba yanayin aiki.
Ma’aikatan sun zargi hukumar gudanarwar majalisar dokokin kasar da karya yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da suka shiga da kungiyar a ranar 13 ga Afrilu, 2021 kan cikakken aiwatar da sabuwar dokar mafi karancin albashi na kasa na shekarar 2019 da kuma yanayin aiki.
Da ya ke jawabi ga ma’aikatan, shugaban kungiyar ta PASAN, Sabiyi Sunday, ya ce, “Shugabannin kungiyar za su halarci wani taron gaggawa da hukumar Kula da ma’aikata ta kasa ta kira, domin magance matsalolin da ma’aikatan mu”.