fidelitybank

Mutane 19 sun mutu yayin da 26 suka jikkata a Kano – FRSC

Date:

A kalla mutane 19 ne suka mutu yayin da wasu 26 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya auku a Bagauda kusa da harabar makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya da ke kan hanyar Kano zuwa Zaria.

Kwamandan hukumar kare aukuwar hadura ta kasa FRSC a jihar Kano, Zubairu Mato, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ranar Alhamis a Kano.

Ya ce, hadarin ya rutsa da motocin Hiace guda biyu na kasuwanci mai lamba KBT 152 XA da NSR 275 ZX.

“Mun samu kira da misalin karfe 7:30 na safiyar ranar 6 ga Janairu, 2022. Da samun labarin, mun yi gaggawar aika jami’an mu da motar mu zuwa wurin da lamarin ya faru, domin ceto wadanda abin ya shafa da karfe 7:40 na safe,” in ji Mato.

Kwamandan sashin ya ce, hatsarin ya auku ne, sakamakon gudun wuce kima, lamarin da ya kai ga karo da juna inda motocin biyu suka yi taho mu gama da wuta. Hatsarin ya shafi jimillar fasinjoji 45 a cikin motocin bas guda biyu, daga cikinsu maza 14 da mata hudu sai wani yaro namiji daya da suka rasa rayukansu yayin da wasu 26 suka samu munanan raunuka,” inji shi.

Mato ya ce,”An kai wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kura, domin yi musu magani, yayin da a ka mika gawarwakin sauran ga ‘yan uwansu da ke ofishin ‘yan sanda na Bebeji”. A cewar Mato.

Kwamandan sashen ya shawarci masu ababen hawa da su guji yin gudu, kima a kan ababen hawan su.

 

dailypostnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp