A kalla mutane 19 ne suka mutu yayin da wasu 26 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya auku a Bagauda kusa da harabar makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya da ke kan hanyar Kano zuwa Zaria.
Kwamandan hukumar kare aukuwar hadura ta kasa FRSC a jihar Kano, Zubairu Mato, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ranar Alhamis a Kano.
Ya ce, hadarin ya rutsa da motocin Hiace guda biyu na kasuwanci mai lamba KBT 152 XA da NSR 275 ZX.
“Mun samu kira da misalin karfe 7:30 na safiyar ranar 6 ga Janairu, 2022. Da samun labarin, mun yi gaggawar aika jami’an mu da motar mu zuwa wurin da lamarin ya faru, domin ceto wadanda abin ya shafa da karfe 7:40 na safe,” in ji Mato.
Kwamandan sashin ya ce, hatsarin ya auku ne, sakamakon gudun wuce kima, lamarin da ya kai ga karo da juna inda motocin biyu suka yi taho mu gama da wuta. Hatsarin ya shafi jimillar fasinjoji 45 a cikin motocin bas guda biyu, daga cikinsu maza 14 da mata hudu sai wani yaro namiji daya da suka rasa rayukansu yayin da wasu 26 suka samu munanan raunuka,” inji shi.
Mato ya ce,”An kai wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kura, domin yi musu magani, yayin da a ka mika gawarwakin sauran ga ‘yan uwansu da ke ofishin ‘yan sanda na Bebeji”. A cewar Mato.
Kwamandan sashen ya shawarci masu ababen hawa da su guji yin gudu, kima a kan ababen hawan su.