fidelitybank

Mutane 19 sun mutu yayin da 26 suka jikkata a Kano – FRSC

Date:

A kalla mutane 19 ne suka mutu yayin da wasu 26 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya auku a Bagauda kusa da harabar makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya da ke kan hanyar Kano zuwa Zaria.

Kwamandan hukumar kare aukuwar hadura ta kasa FRSC a jihar Kano, Zubairu Mato, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ranar Alhamis a Kano.

Ya ce, hadarin ya rutsa da motocin Hiace guda biyu na kasuwanci mai lamba KBT 152 XA da NSR 275 ZX.

“Mun samu kira da misalin karfe 7:30 na safiyar ranar 6 ga Janairu, 2022. Da samun labarin, mun yi gaggawar aika jami’an mu da motar mu zuwa wurin da lamarin ya faru, domin ceto wadanda abin ya shafa da karfe 7:40 na safe,” in ji Mato.

Kwamandan sashin ya ce, hatsarin ya auku ne, sakamakon gudun wuce kima, lamarin da ya kai ga karo da juna inda motocin biyu suka yi taho mu gama da wuta. Hatsarin ya shafi jimillar fasinjoji 45 a cikin motocin bas guda biyu, daga cikinsu maza 14 da mata hudu sai wani yaro namiji daya da suka rasa rayukansu yayin da wasu 26 suka samu munanan raunuka,” inji shi.

Mato ya ce,”An kai wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kura, domin yi musu magani, yayin da a ka mika gawarwakin sauran ga ‘yan uwansu da ke ofishin ‘yan sanda na Bebeji”. A cewar Mato.

Kwamandan sashen ya shawarci masu ababen hawa da su guji yin gudu, kima a kan ababen hawan su.

 

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp