Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta dauko gawar wani mutum a ranar Litinin.
An fito da gawar ne daga tankin dizal a wani kamfani dake karamar hukumar Kumbotso.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara, Saminu Abdullahi ya bayyana cewa mamacin na da jarkar a hannunsa.
Kakakin ya ce hukumar ta amsa kiran gaggawar da mazauna yankin suka yi musu.
Likitan ne ya tabbatar da mutuwar mutumin bayan an mika gawar ga ofishin ‘yan sanda na Panshekara da ke Kano.
Abdullahi ya kara da cewa “Kokarin gano shi ya ci tura saboda jami’an tsaro a kamfanin sun ce ba su san shi ba.”