fidelitybank

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Date:

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban birnin ƙasar, Abuja, inda ta yi kira ga mazauna birnin su cigaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin lumana.

Gwamnatin Najeriya ta bayyana haka ne a matsayin martani ga gargaɗin tsaro da Amurka ta aika zuwa ga ƴanƙasarta da ke birnin Abuja.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Ministan Watsa Labarai na Najeriya, Mohammed Idris ya fitar, inda a ciki ya ce, “gwamnatin Najeriya ta samu labarin gargaɗin da Amurka ta aika wa ma’aikatan ofishin jakadancinta da ma ƴanƙasarta da ke Abuja game da tsaro.

“Duk da gwamnatin Najeriya na girmama haƙƙin da ofisoshin jakadanci – ciki har da na Amurka – ke da shi na ba ƴanƙasarta shawara ko gargaɗi game da matsalolin tsaro, yana da muhimmanci mu tabbatar da cewa babu wata barazanar tsaro da Najeriya ke fuskanta, sannan mazauna birnin da masu ziyara babu wata barazana da suke fuskanta.”

Sanarwar ta ƙara da cewa akwai cikakken tsaro a Abuja, “domin jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da daƙile dukkan wata barazanar tsaro.”

nnn hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...

Da Ɗumi-Ɗumi: Kashim Shettima zai rako gawar Muhammadu Buhari zuwa Najeriya

Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu. Ya rasu ne...

Ina Tinubu ya ke ya ɓata ba bayani – ADC

Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba,...

Koriya ta Arewa za ta ba Rasha ƙarin sojoji domin yaƙin Ukraine

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya yi...

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya...

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya...

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...
X whatsapp