Dakarun rundunar Operation Hadin Kai na sojojin Najeriya, sun tabbatar da hallaka mutanen da suka kira ‘yan ta’adda 37 a yankin Arewa maso Yamma tare da kama wasu 17.
Daraktan yaɗa labarai na rundunar sojin Najeriya, Manjo Janar Benard Onyeuko ne ya bayyana hakan yayin jawabinsa game da ayyukan rundunar a mako biyu da suka wuce a Abuja ranar Alhamis.
Ya ce“Dakarun sun kashe ‘yan fashin daji 12, sannan sun kama 15 cikin mako biyu da suka gabata, tare da ƙwace makamai 21 da ƙunshin harsasai 117 iri daban-daban, ciki har da mota mai bindiga huɗu daga hannun mutanen”.
“Mun yi nasarar ceto mutum 16 da aka yi garkuwa da su, yayin da “ƴan ta’addan” 863 da iyalansu suka miƙa wuya. Mun kai hare-hare kan ‘yan ta’adda da ‘yan fashin daji da sauran miyagu a dukkan sansanoni da ke faɗin ƙasa cikin mako biyu da suka wuce, inda muka samu kyakkyawan sakamako,” in ji Manjo Janar Benard.