fidelitybank

Mun kama mutanen da ake zargi da kashe yarinya a Kano – SP Kiyawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta tabbatar da kama mutanen da ake zargi da kashe wata yarinya mai suna Hanifa, ‘yar shekara biyar da haihuwa.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda jihar Kano, SP Abdullahi Kiyawa ne ya tabbatar da hakan ga manema labarai a ranar Alhamis.

ya ce,”An gano gawar ta cewa, jim kaɗan bayan sace Hanifa sai ɓarayin suka kira iyayenta suna neman kuɗin fansa har kimanin Naira miliyan shida”.

“Bayan samun rahoton ne sai kwamishinan ƴan sanda na jihar, CP Sama’ila ya haɗa taron gaggawa na manyan shugabannin tsaro, domin gano ƙrin dabarun tabbatar da tsaro a jihar Kano. A na zargin malamin makarantar su Hanifa ne ya sace ta ya kashe ta sannan ya binne gawarta a cikin makarantar, daga nan kuma sai rundunar ƴan sanda ta tayar da tawagar Kan ka ce Kwabo, wato Operation Puff Ader, domin tabbatar da kamo waɗanda suka sace yarinyar”.

“Da aka ci gaba da bibiya aka yi ta aiki da har nasara ta kai aka kama mutum biyu da farko, wato Abdulmalik Muhammad Tanko mai shekara 30 da abokinsa Hashim Isiyaku mai shekara 37 da suke unguwar Tudun Murtala, kuma jami’an DSS suka yi nasarar kama su,” in ji DSP Abdullahi Haruna Kiyawa.

“Daga binciken da aka fara ne Abdulmalik ya tabbatar da cewa Hanifa dalibarsa ce ta na karatu a makarantar da yake koyarwa a Kwanar Dakata. Ya sace ta ne ya kai ta gidansa ya ɓoye ta har kimanin sati biyu, ya kuma nemi a ba shi kuɗi har Naira miliyan shida.

“Ranar 18 ga watan 12 da ya fahimci ana so a gano cewa yarinyar tana tare da shi, don har gidansa ana ta bibiya an je, sai ya gaya mana (ƴan sanda) cewa ya ba ta guba ta sha ta mutu.

“Daga nan sai suka haɗa baki da wancan abokin na sa Hashim suka ɗauke ta suka sa a buhu suka kai ta wannan makarantar suka yi tono suka binne ta” .

DSP Kiyawa ya ƙara da cewa “sai a yau 20 ga watan Janairun 2021 ne mu ka yi nasarar kamo su”. A cewar SP Kiyawa.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuƙuru wajen daƙile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta ɗauki ɗan wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen ɗan wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp