Majalisar taimakawa a bangaren shari’a ta kasa reshen jihar Kano, ta ce ta karbi korafe-korafen shari’u na mutane 292 a bara.
Ko’odinetan majalisar, Labaran Kabo ne ya bayyana haka a zantawarsa da manema labarai a ranar Lahadi a Kano.
Ya ce, daga cikin shari’o’in 292, akwai 232 na kan laifuka ne yayin da 60 kuma na fararen hula ne.
ya kuma ce, “Laifukan sun hada da kisan kai, fyade, fashi da makami, karya amana, da kuma sata, yayin da shari’ar farar hula ta shafi aure, gado, rikicin filaye da karbo bashi,” inji shi.
Kabo ya kara da cewa, a tsawon lokacin da majalisar ta kammala tantance kararraki 69 yayin da 223 ke ci gaba da shari’a a kotuna.
“Hukumar mu ita ce tabbatar da daidaito da adalci ga dukkan ‘yan Najeriya ta hanyar ba da tallafin shari’a kyauta da taimako ta hanyar da ke nuna ainihin manufofin tsarin mulki da manufofin gwamnati na samun adalci,” in ji shi.
A cewarsa, majalisar ta na ba da ‘yanci ga kowa. Ya kuma shawarci wadanda ba za su iya biyan kudi wajen daukan lauya da su tuntube su.