fidelitybank

Mun karbi shari’u 292 a shekarar da ta gabata a Kano – Labaran Kabo

Date:

Majalisar taimakawa a bangaren shari’a ta kasa reshen jihar Kano, ta ce ta karbi korafe-korafen shari’u na mutane 292 a bara.

Ko’odinetan majalisar, Labaran Kabo ne ya bayyana haka a zantawarsa da manema labarai  a ranar Lahadi a Kano.

Ya ce, daga cikin shari’o’in 292, akwai 232 na kan laifuka ne yayin da 60 kuma na fararen hula ne.

ya kuma ce, “Laifukan sun hada da kisan kai, fyade, fashi da makami, karya amana, da kuma sata, yayin da shari’ar farar hula ta shafi aure, gado, rikicin filaye da karbo bashi,” inji shi.

Kabo ya kara da cewa, a tsawon lokacin da majalisar ta kammala tantance kararraki 69 yayin da 223 ke ci gaba da shari’a a kotuna.

“Hukumar mu ita ce tabbatar da daidaito da adalci ga dukkan ‘yan Najeriya ta hanyar ba da tallafin shari’a kyauta da taimako ta hanyar da ke nuna ainihin manufofin tsarin mulki da manufofin gwamnati na samun adalci,” in ji shi.

A cewarsa, majalisar ta na ba da  ‘yanci ga kowa. Ya kuma shawarci wadanda ba za su iya biyan kudi wajen daukan lauya da su tuntube su.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp