fidelitybank

Mun fara shirin tsawaita rayuwar al’ummar Nijeriya — NSCC

Date:

 

Wata sabuwar hukuma mai suna Cibiyar Kula da Tsofaffi ta Ƙasa, NSCC, ta ci alwashin ɓullo da shirye-shirye da za su tsawaita rayuwar al’ummar Nijeriya, wanda a turance a ke kira da ‘life expectancy’.

Darakta Janar ta cibiyar, Emem Omokaro ce ta baiyana hakan a wata ganawa da Kanfanin Daillancin Labarai, NAN a jiya Lahadi a Abuja.

Omokaro ta ƙara da cewa cibiyar za ta bunƙasa rayuwar tsufa har ta zama abar sha’awa a Nijeriya.

A cewar Omokaro a shekarar 2015 da 2018, Nijeriya tana ta can ƙasa a jerin ƙasashe masu tsayin rayuwa na duniya sabo da a lokacin babu wasu ajiyayyun bayanai da zai sanya ta kasance a saman jerin sunayen.

“A na yin jerin sunayen ne ta hanyar duba da irin kula da kuma jin daɗi da tsofaffi ke samu a ƙasa, da kuma wasu matakai da su ke yin nuni da hakan, misali, wa’adin tsawon rayuwa na tsofaffin mutane da dai sauran matakai.

“A Nijeriya, mutane su ke kaiwa shekaru 60, in ma sun kai, mutane nawa ne ke samun cikakkiyar lafiya da rayuwa bayan shekara 60 ɗin. Nawa ne a cikinsu su ke samun inshorar rayuwa da kuma kuɗaɗen kashewa?

“Amma yanzu, da zuwan NSCC, wa’adin tsawon al’ummar Nijeriya zai ƙaru sabo da a yanzu muna da Doka ta Shekaru a Nijeriya. Mun tanadi wani kundin tsari na tsawon shekaru 10 sannan kuma dokar da ta kafa NSCC za ta taimaka gudanar da shirin,” in ji Omokaro.

Ta ƙara da cewa” kwanan nan tsawon wa’adin shekarun ƴan Nijeriya zai ƙaru sabo da shirye-shiryen da mu ka tanada za su sanya ƴan Nijeriya su samu tsawon rai, za kuma a ƙarawa tsofaffi kulawa ta musamman,” in ji ta.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...
X whatsapp