fidelitybank

Mun fara shirin tsawaita rayuwar al’ummar Nijeriya — NSCC

Date:

 

Wata sabuwar hukuma mai suna Cibiyar Kula da Tsofaffi ta Ƙasa, NSCC, ta ci alwashin ɓullo da shirye-shirye da za su tsawaita rayuwar al’ummar Nijeriya, wanda a turance a ke kira da ‘life expectancy’.

Darakta Janar ta cibiyar, Emem Omokaro ce ta baiyana hakan a wata ganawa da Kanfanin Daillancin Labarai, NAN a jiya Lahadi a Abuja.

Omokaro ta ƙara da cewa cibiyar za ta bunƙasa rayuwar tsufa har ta zama abar sha’awa a Nijeriya.

A cewar Omokaro a shekarar 2015 da 2018, Nijeriya tana ta can ƙasa a jerin ƙasashe masu tsayin rayuwa na duniya sabo da a lokacin babu wasu ajiyayyun bayanai da zai sanya ta kasance a saman jerin sunayen.

“A na yin jerin sunayen ne ta hanyar duba da irin kula da kuma jin daɗi da tsofaffi ke samu a ƙasa, da kuma wasu matakai da su ke yin nuni da hakan, misali, wa’adin tsawon rayuwa na tsofaffin mutane da dai sauran matakai.

“A Nijeriya, mutane su ke kaiwa shekaru 60, in ma sun kai, mutane nawa ne ke samun cikakkiyar lafiya da rayuwa bayan shekara 60 ɗin. Nawa ne a cikinsu su ke samun inshorar rayuwa da kuma kuɗaɗen kashewa?

“Amma yanzu, da zuwan NSCC, wa’adin tsawon al’ummar Nijeriya zai ƙaru sabo da a yanzu muna da Doka ta Shekaru a Nijeriya. Mun tanadi wani kundin tsari na tsawon shekaru 10 sannan kuma dokar da ta kafa NSCC za ta taimaka gudanar da shirin,” in ji Omokaro.

Ta ƙara da cewa” kwanan nan tsawon wa’adin shekarun ƴan Nijeriya zai ƙaru sabo da shirye-shiryen da mu ka tanada za su sanya ƴan Nijeriya su samu tsawon rai, za kuma a ƙarawa tsofaffi kulawa ta musamman,” in ji ta.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp