fidelitybank

Mun fara shirin tsawaita rayuwar al’ummar Nijeriya — NSCC

Date:

 

Wata sabuwar hukuma mai suna Cibiyar Kula da Tsofaffi ta Ƙasa, NSCC, ta ci alwashin ɓullo da shirye-shirye da za su tsawaita rayuwar al’ummar Nijeriya, wanda a turance a ke kira da ‘life expectancy’.

Darakta Janar ta cibiyar, Emem Omokaro ce ta baiyana hakan a wata ganawa da Kanfanin Daillancin Labarai, NAN a jiya Lahadi a Abuja.

Omokaro ta ƙara da cewa cibiyar za ta bunƙasa rayuwar tsufa har ta zama abar sha’awa a Nijeriya.

A cewar Omokaro a shekarar 2015 da 2018, Nijeriya tana ta can ƙasa a jerin ƙasashe masu tsayin rayuwa na duniya sabo da a lokacin babu wasu ajiyayyun bayanai da zai sanya ta kasance a saman jerin sunayen.

“A na yin jerin sunayen ne ta hanyar duba da irin kula da kuma jin daɗi da tsofaffi ke samu a ƙasa, da kuma wasu matakai da su ke yin nuni da hakan, misali, wa’adin tsawon rayuwa na tsofaffin mutane da dai sauran matakai.

“A Nijeriya, mutane su ke kaiwa shekaru 60, in ma sun kai, mutane nawa ne ke samun cikakkiyar lafiya da rayuwa bayan shekara 60 ɗin. Nawa ne a cikinsu su ke samun inshorar rayuwa da kuma kuɗaɗen kashewa?

“Amma yanzu, da zuwan NSCC, wa’adin tsawon al’ummar Nijeriya zai ƙaru sabo da a yanzu muna da Doka ta Shekaru a Nijeriya. Mun tanadi wani kundin tsari na tsawon shekaru 10 sannan kuma dokar da ta kafa NSCC za ta taimaka gudanar da shirin,” in ji Omokaro.

Ta ƙara da cewa” kwanan nan tsawon wa’adin shekarun ƴan Nijeriya zai ƙaru sabo da shirye-shiryen da mu ka tanada za su sanya ƴan Nijeriya su samu tsawon rai, za kuma a ƙarawa tsofaffi kulawa ta musamman,” in ji ta.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...
X whatsapp