Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce, an rufe dukannin sansanonin ƴan gudun hijira da ke jihar.
Gwamnan ya bayyana haka ne a saƙon murnar sabuwar shekara da ya fitar, inda ya ce, matakin da a ka ɗauka na rufe dukannin sansanonin an ɗauke shi ne, domin ƙara inganta rayuwar jama’a.
A makon da ya gabata, ƙungiyoyin kare haƙƙin bil Adama sun roƙi hukumomi da su janye wannan kudirin na su, sakamakon gwamnati ba ta da tabbaci na kula da haƙƙoƙin ƴan gudun hijira.
Ƙungiyoyin sun yi gargaɗin cewa, yunƙurin da a ke yi na mayar da ƴan gudun hijira muhallansu zai sa rayukan sama da iyalai 10,000 cikin hatsari, sakamakon irin hare-haren da ƴan Boko Haram da ƴan ISWAP ke ci gaba da kai wa da kuma zargin cin zarafi da sojoji ke yi.
Sai dai Gwamna Zulum ya dage kan cewa, sansanonin sun soma zama wurare da ake aikata munanan abubuwa iri-iri, ciki har da karuwanci da sayar da miyagun ƙwayoyi da kuma daba a wasu lokutan.
BBC ta rawaito cewa, sama da ƴan gudun hijira miliyan 1.8 ne a ka mayar garuruwan su domin ci gaba da gudanar da rayuwarsu.