fidelitybank

Mu na da hujja a kan rufe sansanin ‘yan gudun hijira – Zulum

Date:

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ce, an rufe dukannin sansanonin ƴan gudun hijira da ke jihar.

Gwamnan ya bayyana haka ne a saƙon murnar sabuwar shekara da ya fitar, inda ya ce, matakin da a ka ɗauka na rufe dukannin sansanonin an ɗauke shi ne, domin ƙara inganta rayuwar jama’a.

A makon da ya gabata, ƙungiyoyin kare haƙƙin bil Adama sun roƙi hukumomi da su janye wannan kudirin na su, sakamakon gwamnati ba ta da tabbaci na kula da haƙƙoƙin ƴan gudun hijira.

Ƙungiyoyin sun yi gargaɗin cewa, yunƙurin da a ke yi na mayar da ƴan gudun hijira muhallansu zai sa rayukan sama da iyalai 10,000 cikin hatsari, sakamakon irin hare-haren da ƴan Boko Haram da ƴan ISWAP ke ci gaba da kai wa da kuma zargin cin zarafi da sojoji ke yi.

Sai dai Gwamna Zulum ya dage kan cewa, sansanonin sun soma zama wurare da ake aikata munanan abubuwa iri-iri, ciki har da karuwanci da sayar da miyagun ƙwayoyi da kuma daba a wasu lokutan.

BBC ta rawaito cewa, sama da ƴan gudun hijira miliyan 1.8 ne a ka mayar garuruwan su domin ci gaba da gudanar da rayuwarsu.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp