fidelitybank

Mu kungiyoyi ne na duniya da dangogin mu dake tallafa mana – IPOB

Date:

Haramtacciyar kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) a ranar Talata ta ce magoya bayanta na gida da na waje sun kasance tushen daukar nauyin su.

Sakatariyar yada labaran kungiyar, Emma Powerful ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce, “A karo na goma sha uku, babu wani mutum daya da zai iya daukar nauyin kungiyar IPOB. Mu ƙungiyoyi ne na duniya kuma miliyoyin dangin mu a gida da waje sun kasance tushen tallafin mu.

“Ba mu taba boye wannan gaskiyar ba, saboda mu ba kungiya ce ta sirri ko ta’addanci ba. IPOB ta na da tushe mai kyau kuma ba ma bukatar wani Okorocha ko Uche Nwosu ko Hope Uzodinma ko wani dan siyasa kan lamarin ya dauki nauyin mu. Ba mu da mu’amala da gurbatattun ‘yan siyasa da mutanen da ke da shakku kan tushen arzikin su.” inji IPOB.

In za a iya tunawa cewa, IPOB kungiya ce mai fafutukar neman ballewa a Najeriya, babban burinta shi ne dawo da kasar Biafra mai cin gashin kanta a tsohon yankin Gabashin Najeriya, wanda ya kunshi yankunan Kudu maso Gabas da Kudu-maso-Kudu a yau; ta hanyar zaben raba gardama na ‘yancin kai.

An kafa kungiyar ne a shekarar 2012 a hannun Nnamdi Kanu, dan gwagwarmayar siyasar Najeriya dan kasar Birtaniya wanda ya yi fice wajen fafutukar neman ‘yancin kasar Biafra.

punch newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...
X whatsapp