fidelitybank

Mu kungiyoyi ne na duniya da dangogin mu dake tallafa mana – IPOB

Date:

Haramtacciyar kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) a ranar Talata ta ce magoya bayanta na gida da na waje sun kasance tushen daukar nauyin su.

Sakatariyar yada labaran kungiyar, Emma Powerful ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce, “A karo na goma sha uku, babu wani mutum daya da zai iya daukar nauyin kungiyar IPOB. Mu ƙungiyoyi ne na duniya kuma miliyoyin dangin mu a gida da waje sun kasance tushen tallafin mu.

“Ba mu taba boye wannan gaskiyar ba, saboda mu ba kungiya ce ta sirri ko ta’addanci ba. IPOB ta na da tushe mai kyau kuma ba ma bukatar wani Okorocha ko Uche Nwosu ko Hope Uzodinma ko wani dan siyasa kan lamarin ya dauki nauyin mu. Ba mu da mu’amala da gurbatattun ‘yan siyasa da mutanen da ke da shakku kan tushen arzikin su.” inji IPOB.

In za a iya tunawa cewa, IPOB kungiya ce mai fafutukar neman ballewa a Najeriya, babban burinta shi ne dawo da kasar Biafra mai cin gashin kanta a tsohon yankin Gabashin Najeriya, wanda ya kunshi yankunan Kudu maso Gabas da Kudu-maso-Kudu a yau; ta hanyar zaben raba gardama na ‘yancin kai.

An kafa kungiyar ne a shekarar 2012 a hannun Nnamdi Kanu, dan gwagwarmayar siyasar Najeriya dan kasar Birtaniya wanda ya yi fice wajen fafutukar neman ‘yancin kasar Biafra.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...

Mayakan IS sun yi wa Sojojin Najeriya barna a kwana biyu

Mayaƙan IS sun ƙara kai wa sojojin Najeriya hari,...
X whatsapp