Kamfanin sadarwa mafi girma a Afirka MTN ya sanar da cewa wajibi ne ma’aikatansa su yi allurar rigakafin korona daga watan Janairu mai zuwa.
Sai dai kamfanin mai Shelkwata a Afirka ta Kudu ya ce, ba za a tilasta wa masu cikakken uzuri ba.
Cikin wata sanarwar da ya fitar, ya ce”Ma’aikatan da ba su da wani dalili na ƙin yin rigakafin, amma suka ƙi zuwa a yi musu, ba lallai ne MTN ya ci gaba da aiki da su ba,” a cewar MTN.
BBC ta rawaito cewa MTN shi ne kamfani mafi girma da ya ayyana aniyarsa ta soke kwantiragin ma’aikatansa da ba su yi rigakafi ba ya zuwa yanzu, a cewar kamfanin labarai na Bloomberg.