Rundunar tsaro ta Bijilante a yankin unguwar Gaida a karamar hukumar Kumbotso a jihar Kano, ta samu nasarar kama wani matashi mai suna Mustapha, da satar kofa Kyaure a wani gida da a ke kokarin ginawa a yankin.
Dubun matashin ta cika ne a lokacin da makwabcin da ya ke kusa da kangon ya fito da sanyin Asuba ya kama matashin.
Daga nan kuma ya mika shi zuwa wajen kungiyar Bijilanten yankin, domin daukar mataki a kansa.
Sai dai wanda a ke zargin mai suna Mustapha, ya ce,” Wannan ne karo na farko da na fara daukar kofar mutane, nib a sana’a ta ba ce, kuma wannan shi ne na karshe b azan kara yi ba, na dauki kofar ne domin na siyar na yi bukatun kai na da kudaden da zarar na sayar da kofar”. Inji Mustapha.
A nasa jawabin Kwamandan Bijilanten yankin unguwar Gaida, Shekarau Aliyu Cinnaka ba ka san na gida ba, ya ce,” Za mu dauki mataki a kansa zuwa wajen hukuma, domin daukar mataki na gaba, wajen hana faruwar abun”. A cewar Shekarau.