Zainab Marwa, wadda ita ce matar shugaban hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA), Buba Marwa ta rasu a ranar Asabar dinnan.
Sanarwar da dangin ta fitar ta ce Zainab ta rasu ne da sanyin safiyar Asabar, bayan ta yi fama da gajeruwar rashin lafiya.
Zainab Marwa ta rasu ta na da shekaru 66 a duniya.
Marigayiya Zainab ta bar ‘ya’yanta hudu, ciki akwai Abubakar da Muhammed da Maryam da kuma Zainab, tare da jikoki 10 da kuma ‘yan uwanta da mahaifiyarta.