fidelitybank

Mata su rungumi hadin kai gabannin 2023 – Aisha Buhari

Date:

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari, ta gargadi ‘yan uwanta mata da su rungumi hadin kai gabanin babban zabe na 2023.

Naija News ta rawaito cewa, Uwargidan shugaban kasar ta ba da shawarar ne a ranar Litinin yayin da ta ke karbar bakwancin mataimakin shugaban Laberiya, Jewel Howard-Taylor.

Mataimakiyar ta ziyarci Najeriya ne, domin halartar babban taron mata na jam’iyyar APC na kasa.

Da ta ke jawabi a wajen taron, Aisha Buhari ta ji dadin ‘yan jam’iyyar APC da ke kan iyakokin kasar da su yi amfani da sabbin dabaru, domin tabbatar da cewa mata da yawa sun shiga cikin yanke shawara.

Ta kuma jaddada cewa, hadin kan matan zai taimaka musu wajen yin tasiri mai karfi a harkokin zabe.

Uwargidan shugaban Najeriyar ta kuma bukaci masu ruwa da tsaki da su tallafa wa jinsin mata, domin cimma bukatar su na kara shiga harkokin siyasa. Ta ce: “Akwai bukatar a karfafa mata gwiwa, domin su kara shiga harkokin siyasa, kuma kasar na bukatar shigar mu. Ya zama dole mu sanya ido kan yadda za mu yi aiki tare, domin hada kan mata a yakin neman zabe mai zuwa gabanin zaben 2023.”

Aisha ta kara da cewa “Na gamsu cewa tarihinki a matsayinki na tsohuwar uwargidan shugaban kasar Laberiya, kuma kwararriya kan harkokin siyasa zai kara kima a taron”. In ji Aisha

Da take yabawa kasancewar Howard-Taylor a wurin taron, Misis Buhari ta ce, kalaman za su karawa mata kwarin gwiwar halartar taron.

 

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp