Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari, ta gargadi ‘yan uwanta mata da su rungumi hadin kai gabanin babban zabe na 2023.
Naija News ta rawaito cewa, Uwargidan shugaban kasar ta ba da shawarar ne a ranar Litinin yayin da ta ke karbar bakwancin mataimakin shugaban Laberiya, Jewel Howard-Taylor.
Mataimakiyar ta ziyarci Najeriya ne, domin halartar babban taron mata na jam’iyyar APC na kasa.
Da ta ke jawabi a wajen taron, Aisha Buhari ta ji dadin ‘yan jam’iyyar APC da ke kan iyakokin kasar da su yi amfani da sabbin dabaru, domin tabbatar da cewa mata da yawa sun shiga cikin yanke shawara.
Ta kuma jaddada cewa, hadin kan matan zai taimaka musu wajen yin tasiri mai karfi a harkokin zabe.
Uwargidan shugaban Najeriyar ta kuma bukaci masu ruwa da tsaki da su tallafa wa jinsin mata, domin cimma bukatar su na kara shiga harkokin siyasa. Ta ce: “Akwai bukatar a karfafa mata gwiwa, domin su kara shiga harkokin siyasa, kuma kasar na bukatar shigar mu. Ya zama dole mu sanya ido kan yadda za mu yi aiki tare, domin hada kan mata a yakin neman zabe mai zuwa gabanin zaben 2023.”
Aisha ta kara da cewa “Na gamsu cewa tarihinki a matsayinki na tsohuwar uwargidan shugaban kasar Laberiya, kuma kwararriya kan harkokin siyasa zai kara kima a taron”. In ji Aisha
Da take yabawa kasancewar Howard-Taylor a wurin taron, Misis Buhari ta ce, kalaman za su karawa mata kwarin gwiwar halartar taron.