fidelitybank

Mata su rungumi hadin kai gabannin 2023 – Aisha Buhari

Date:

Uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari, ta gargadi ‘yan uwanta mata da su rungumi hadin kai gabanin babban zabe na 2023.

Naija News ta rawaito cewa, Uwargidan shugaban kasar ta ba da shawarar ne a ranar Litinin yayin da ta ke karbar bakwancin mataimakin shugaban Laberiya, Jewel Howard-Taylor.

Mataimakiyar ta ziyarci Najeriya ne, domin halartar babban taron mata na jam’iyyar APC na kasa.

Da ta ke jawabi a wajen taron, Aisha Buhari ta ji dadin ‘yan jam’iyyar APC da ke kan iyakokin kasar da su yi amfani da sabbin dabaru, domin tabbatar da cewa mata da yawa sun shiga cikin yanke shawara.

Ta kuma jaddada cewa, hadin kan matan zai taimaka musu wajen yin tasiri mai karfi a harkokin zabe.

Uwargidan shugaban Najeriyar ta kuma bukaci masu ruwa da tsaki da su tallafa wa jinsin mata, domin cimma bukatar su na kara shiga harkokin siyasa. Ta ce: “Akwai bukatar a karfafa mata gwiwa, domin su kara shiga harkokin siyasa, kuma kasar na bukatar shigar mu. Ya zama dole mu sanya ido kan yadda za mu yi aiki tare, domin hada kan mata a yakin neman zabe mai zuwa gabanin zaben 2023.”

Aisha ta kara da cewa “Na gamsu cewa tarihinki a matsayinki na tsohuwar uwargidan shugaban kasar Laberiya, kuma kwararriya kan harkokin siyasa zai kara kima a taron”. In ji Aisha

Da take yabawa kasancewar Howard-Taylor a wurin taron, Misis Buhari ta ce, kalaman za su karawa mata kwarin gwiwar halartar taron.

 

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...
X whatsapp