A yau ne ake sa ran sake gurfanar da jagoran ƴan awaren Biafra, Nnamdi Kanu da sabbin tuhume-tuhume 15 na ta’addanci a gaban kotu.
Sabbin tuhume-tuhumen wadanda aka gabatar da su ranar Litinin sun zo ne ƙasa da sa’o’i 24 kafin a sake shiga kotu a ci gaba da shari’ar da ake yi masa.
Nnamdi Kanu zai sake gurfana a kotun Abuja, bisa tuhumar cin amanar ƙasa da ta’addanci, da kafa haramtacciyar ƙungiya, laifukan da hukuncinsu hukuncin kisa ne idan sun tabbata.
Wannan ne karo na biyu da gwamnati ke yin kwaskwarima kan tuhume-tuhumen da ake yi wa jagoran na ƙungiyar IPOB.
An fara kama Kanu ne a 2015, bisa tuhume-tuhimen ta’addanci da jagorantar haramtaciyyar ƙungiya da wallafa munanan kalamai, da mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma shigar da miyagun kaya ƙasar ta Najeriya.
Nnamdi Kanu wanda ya ke da fasfo na ƙasar Birtaniya, kuma ya daɗe a ƙasar, sannan an mai da shi Najeriya, to amma har yanzu gwamnati ba ta bayyana daga wata ƙasa aka tissa ƙeyarsa ba.